< Habakkuk 3 >

1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
Molitev preroka Habakúka na Šiginot.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
Oh Gospod, slišal sem tvoj govor in bil sem prestrašen. Oh Gospod, oživi svoje delo v sredi let, v sredi let ga daj spoznati, v besu se spomni usmiljenja.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
Bog je prišel iz Temána in Sveti z gore Parán. (Sela) Njegova slava je pokrila nebo in zemlja je bila polna njegove hvale.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
Njegov sijaj je bil kakor svetloba; imel je rogove, izhajajoče iz njegove roke in tam je bilo skrivališče njegove moči.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
Pred njim je odšla kužna bolezen in goreče oglje je šlo naprej ob njegovih stopalih.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
Stal je in izmeril zemljo. Pogledal je in razgnal narode in večne gore so bile razkropljene, starodavni hribi so se upognili. Njegove poti so večne.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
Videl sem kušánske šotore v stiski in zavese midjánske dežele so trepetale.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Mar je bil Gospod nezadovoljen zoper reke? Je bila tvoja jeza zoper reke? Je bil tvoj bes zoper morje, da si jahal na svojih konjih in svojih bojnih vozovih rešitve duš?
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Tvoj lok je bil razgaljen, glede na prisege rodov, celo tvojo besedo. (Sela) Zemljo si oklenil z rekami.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
Gore so te videle in so trepetale, preplavljanje vodá je šlo mimo, globina je izustila svoj glas in svoje roke vzdignila na visoko.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
Sonce in luna sta mirno stala v svojem prebivališču. Ob svetlobi tvojih puščic sta šla in ob siju tvoje lesketajoče sulice.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
V ogorčenju si korakal skozi deželo, pogane si mlatil v jezi.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
Šel si naprej zaradi rešitve duš svojega ljudstva, celó zaradi rešitve duš s svojim maziljenim. Ti raniš poglavarja hiše zlobnih z razkritjem temelja do vratu. (Sela)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
Z njegovimi kopji si prebodel poglavarja njegovih vasi. Ven so prišli kakor vrtinčast veter, da me razkropijo. Njihovo razveseljevanje je bilo kakor, da bi na skrivaj požrli ubogega.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
Skozi morje si hodil s svojimi konji, skozi kup velikih vodá.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
Ko sem slišal, je moj trebuh trepetal, moje ustnice so drgetale ob glasu. Gniloba je vstopila v moje kosti in v sebi sem trepetal, da bi lahko počival na dan stiske. Ko prihaja gor k ljudstvu, jih bo preplavil s svojimi krdeli.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
Čeprav figovo drevo ne bo cvetelo niti ne bo sadu na trtah, [čeprav] bo trud oljke odpovedal in polja ne bodo obrodila nobene hrane; [čeprav] bo trop odrezan od staje in v hlevih ne bo črede,
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
se bom vendar veselil v Gospodu, užival bom v Bogu rešitve moje duše.
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi.
Gospod Bog je moja moč in on bo moja stopala naredil podobna košutinim stopalom in dal mi bo, da hodim na svojih visokih krajih. Vodilnemu pevcu na moja glasbila na strune.

< Habakkuk 3 >