< Habakkuk 3 >

1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
Uma prece de Habakkuk, o profeta, preparada para a música vitoriosa.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
Yahweh, já ouvi falar de sua fama. Estou admirado com seus atos, Yahweh. Renovar seu trabalho no meio dos anos. No meio dos anos, torná-lo conhecido. Na ira, você se lembra da misericórdia.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
Deus veio de Teman, o Santo de Mount Paran. (Selah) Sua glória cobriu os céus, e seus elogios encheram a terra.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
Seu esplendor é como o nascer do sol. Raios brilham de sua mão, onde seu poder está escondido.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
A peste foi antes dele, e a pestilência lhe seguiram os pés.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
Ele ficou de pé, e sacudiu a terra. Ele olhou, e fez as nações tremerem. As antigas montanhas foram desmoronadas. As colinas centenárias desmoronaram. Seus caminhos são eternos.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
Eu vi as tendas de Cushan em aflição. As habitações da terra de Midian tremeram.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Yahweh ficou insatisfeito com os rios? Foi sua raiva contra os rios, ou sua ira contra o mar, que você montou em seus cavalos, em suas carruagens de salvação?
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Você descobriu o seu arco. Você chamou por suas setas juramentadas. (Selah) Você divide a terra com rios.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
As montanhas o viram, e ficaram com medo. Passou a tempestade de águas. O bramido profundo e levantou as mãos para o alto.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
O sol e a lua pararam no céu à luz de suas setas à medida que elas se moviam, ao brilhar de sua lança brilhante.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
Você marchou pela terra em fúria. Você debulhou as nações com raiva.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
Você saiu em busca da salvação de seu povo, para a salvação de seu ungido. Você esmagou a cabeça da terra da maldade. Você os despiu da cabeça aos pés. (Selah)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
Você furou as cabeças de seus guerreiros com suas próprias lanças. Eles vieram como um redemoinho para me dispersar, se gabando como se devorasse os infelizes em segredo.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
Você pisoteou o mar com seus cavalos, agitação de águas poderosas.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
Eu ouvi, e meu corpo tremeu. Meus lábios estremeceram com a voz. A podridão entra em meus ossos, e eu tremo em meu lugar porque devo esperar calmamente pelo dia dos problemas, para a vinda do povo que nos invade.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
Pois mesmo que a figueira não floresça, nem fruta estar na videira, o trabalho da azeitona falha, os campos não produzem alimentos, os rebanhos são cortados da dobra, e não há rebanho nos estábulos,
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
ainda assim, me regozijarei em Yahweh. Eu estarei alegre no Deus da minha salvação!
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.
Yahweh, o Senhor, é minha força. Ele faz meus pés como os pés de veado, e me permite ir em lugares altos. Para o diretor musical, nos meus instrumentos de corda.

< Habakkuk 3 >