< Habakkuk 3 >
1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
Une prière du prophète Habacuc, sur une musique victorieuse.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
Yahvé, j'ai entendu parler de ta renommée. Je suis en admiration devant tes actes, Yahvé. Renouvelez votre travail au milieu des années. Au milieu des années, faites-le savoir. Dans la colère, tu te souviens de la miséricorde.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
Dieu est venu de Teman, le Saint du mont Paran. (Selah) Sa gloire a couvert les cieux, et sa louange a rempli la terre.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
Sa splendeur est comme le lever du soleil. Des rayons brillent de sa main, où son pouvoir est caché.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
La peste l'a précédé, et la peste suivaient ses pas.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
Il se tint debout, et il fit trembler la terre. Il a regardé, et a fait trembler les nations. Les anciennes montagnes se sont effondrées. Les collines séculaires se sont effondrées. Ses voies sont éternelles.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
J'ai vu les tentes de Cushan dans la détresse. Les habitations du pays de Madian ont tremblé.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Les fleuves ont-ils déplu à Yahvé? était votre colère contre les rivières, ou ta colère contre la mer, que vous avez monté sur vos chevaux, sur tes chars de salut?
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Tu as découvert ton arc. Tu as appelé tes flèches assermentées. (Selah) Tu as fendu la terre avec des rivières.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
Les montagnes t'ont vu, et elles ont eu peur. La tempête des eaux est passée. L'abîme a rugi et a levé les mains en l'air.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
Le soleil et la lune étaient immobiles dans le ciel. à la lumière de tes flèches pendant qu'ils partaient, à l'éclat de votre lance étincelante.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
Tu as parcouru le pays avec fureur. Tu as battu les nations dans la colère.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
Tu es sorti pour le salut de ton peuple, pour le salut de tes oints. Tu as écrasé la tête du pays de la méchanceté. Vous les avez déshabillés de la tête aux pieds. (Selah)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
Tu as percé la tête de ses guerriers avec leurs propres lances. Ils sont venus comme un tourbillon pour me disperser, jubilant comme pour dévorer les malheureux en secret.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
Tu as foulé la mer avec tes chevaux, le barattage des eaux puissantes.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
J'ai entendu, et mon corps a tremblé. Mes lèvres ont frémi à la voix. La pourriture entre dans mes os, et je tremble à ma place. car je dois attendre tranquillement le jour de la détresse, pour l'arrivée des gens qui nous envahissent.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
Car même si le figuier ne fleurit pas, ni de fruits dans les vignes, le travail de l'olive échoue, les champs ne produisent pas de nourriture, les troupeaux sont coupés du bercail, et il n'y a pas de troupeau dans les stalles,
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
Mais je me réjouirai en Yahvé. Je serai joyeux dans le Dieu de mon salut!
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.
Yahvé, l'Éternel, est ma force. Il rend mes pieds comme des pieds de cerf, et me permet d'aller dans les hautes sphères. Pour le directeur musical, sur mes instruments à cordes.