< Habakkuk 3 >

1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
A PRAYER of Habakkuk the prophet, set to Shigionoth.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
O LORD, I have heard the report of thee, and am afraid: O LORD, revive thy work in the midst of the years, in the midst of the years make it known; in wrath remember mercy.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
God came from Teman, and the Holy One from mount Paran. (Selah) His glory covered the heavens, and the earth was full of his praise.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
And [his] brightness was as the light; he had rays [coming forth] from his hand: and there was the hiding of his power.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
Before him went the pestilence, and fiery bolts went forth at his feet.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
He stood, and measured the earth; he beheld, and drove asunder the nations: and the eternal mountains were scattered, the everlasting hills did bow; his goings were [as] of old.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
I saw the tents of Cushan in affliction: the curtains of the land of Midian did tremble.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Was the LORD displeased against the rivers? was thine anger against the rivers, or thy wrath against the sea, that thou didst ride upon thine horses, upon thy chariots of salvation?
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
Thy bow was made quite bare; the oaths to the tribes were a [sure] word. (Selah) Thou didst cleave the earth with rivers.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
The mountains saw thee, and were afraid; the tempest of waters passed by: the deep uttered his voice, and lifted up his hands on high.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
The sun and moon stood still in their habitation; at the light of thine arrows as they went, at the shining of thy glittering spear.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
Thou didst march through the land in indignation, thou didst thresh the nations in anger.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
Thou wentest forth for the salvation of thy people, for the salvation of thine anointed; thou woundedst the head out of the house of the wicked, laying bare the foundation even unto the neck. (Selah)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
Thou didst pierce with his own staves the head of his warriors: they came as a whirlwind to scatter me: their rejoicing was as to devour the poor secretly.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
Thou didst tread the sea with thine horses, the heap of mighty waters.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
I heard, and my belly trembled, my lips quivered at the voice; rottenness entered into my bones, and I trembled in my place: that I should rest in the day of trouble, when it cometh up against the people which invadeth him in troops.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
For though the fig tree shall not blossom, neither shall fruit be in the vines; the labour of the olive shall fail, and the fields shall yield no meat; the flock shall be cut off from the fold, and there shall be no herd in the stalls:
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
Yet I will rejoice in the LORD, I will joy in the God of my salvation.
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi.
Jehovah, the Lord, is my strength, and he maketh my feet like hinds’ [feet], and will make me to walk upon mine high places. For the Chief Musician, on my stringed instruments.

< Habakkuk 3 >