< Habakkuk 2 >

1 Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
اکنون از برج دیدبانی خود بالا می‌روم و بر حصار ایستاده، منتظر می‌مانم تا ببینم خداوند به شکایت من چه جواب می‌دهد.
2 Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
آنگاه خداوند به من فرمود: «آنچه را به تو نشان می‌دهم با خطی درشت و خوانا بر تخته سنگی بنویس تا هر کس بتواند با یک نگاه آن را بخواند.
3 Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
اگرچه آنچه به تو نشان می‌دهم در حال حاضر اتفاق نمی‌افتد، ولی مطمئن باش که سرانجام در وقت معین به وقوع خواهد پیوست. هر چند تا وقوع آن، مدت زیادی طول بکشد، ولی منتظر آن باش، زیرا وقوع آن حتمی و بدون تأخیر خواهد بود.
4 “Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
«به کسانی که به خود می‌بالند نگاه کن! این بدکاران نابود خواهند شد، اما عادل به ایمان خواهد زیست.
5 ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol h7585)
به درستی که ثروت، خیانتکار است و این بابِلی‌های متکبر را به دام خواهد انداخت. آنها با حرص و ولع، مانند مرگ، قومها را یکی پس از دیگری به کام خود می‌کشند و اسیر می‌سازند و هرگز سیر نمی‌شوند. (Sheol h7585)
6 “Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
اما زمانی خواهد آمد که همهٔ این اسیرشدگان آنها را تمسخر کرده، خواهند گفت:”ای کسانی که مال و ثروت مردم را به زور از چنگشان درآورده‌اید، اینک به سزای ستمگری‌ها و غارتگری‌های خود می‌رسید.“»
7 Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
ای کسانی که بر دیگران ظلم کرده‌اید، طلبکارانتان ناگهان برخاسته، بر سرتان خواهند ریخت و شما را که درمانده شده‌اید غارت خواهند کرد.
8 Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
بسیاری از قومها را غارت کردید و حال، بقیهٔ قومها شما را غارت خواهند کرد، زیرا خون مردم را ریختید و سرزمینها و شهرها را با مردمش نابود کردید.
9 “Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
وای بر شما که از راههای نادرست ثروت اندوخته‌اید تا زندگی امن و راحتی داشته باشید.
10 Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
وای بر شما که قومها را نابود کرده‌اید، زیرا ننگ و نابودی برای خود به بار آورده‌اید.
11 Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
حتی سنگهای دیوار و تیرهای سقف خانه‌تان بر ضد شما فریاد برمی‌آورند!
12 “Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
وای بر شما که شهرها را با پولی که از راه آدمکشی و غارت به دست آورده‌اید، می‌سازید؛
13 Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
زیرا دارایی خدانشناسان دود شده، به هوا می‌رود و دسترنج آنها نابود می‌گردد. خداوند لشکرهای آسمان چنین مقرر کرده است.
14 Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
همان‌گونه که آبها دریا را پر می‌سازند، زمانی خواهد رسید که درک و شناخت عظمت خداوند، جهان را پر خواهد ساخت.
15 “Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
وای بر شما که همسایگان خود را در زیر ضربه‌هایتان مانند آدمهای مست، بی‌حال و گیج می‌کنید و در آن حال از رسوایی آنها لذت می‌برید.
16 Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
به‌زودی شکوه و جلال خود شما به ننگ و رسوایی تبدیل خواهد شد و شما پیالهٔ داوری خداوند را خواهید نوشید و گیج شده، به زمین خواهید افتاد.
17 Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
جنگلهای لبنان را از بین بردید، اکنون خود شما نابود خواهید شد! حیوانات آنجا را به وحشت انداخته کشتید، پس حال، برای تمام آدمکشی‌ها و ظلم و ستمی که در سرزمینها و شهرها کردید، وحشتزده کشته خواهید شد.
18 “Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
از پرستش بتهایی که به دست انسان ساخته شده‌اند چه فایده‌ای بردید؟ آیا آنها توانستند چیزی به شما یاد دهند؟ چقدر نادان بودید که به ساختهٔ دست خودتان توکل کردید!
19 Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
وای بر آنانی که از بتهای چوبین و بی‌جان خود می‌خواهند که به پا خیزند و ایشان را نجات دهند! و از سنگهای بی‌زبان انتظار دارند که سخن بگویند و ایشان را راهنمایی کنند! بیرون بتها با طلا و نقره پوشانیده شده است، ولی در درونشان نَفَسی نیست.
20 Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.
خداوند در معبد مقدّس خویش است؛ پس تمام جهان در حضور او خاموش باشد.

< Habakkuk 2 >