< Habakkuk 2 >

1 Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
På min vaktpost vil jeg stå og stille mig på varden; og jeg vil skue ut for å se hvad han vil tale til mig, og hvad jeg skal få til svar på mitt klagemål.
2 Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
Og Herren svarte mig og sa: Skriv synet op og skriv det tydelig på tavlene, så det kan leses med letthet!
3 Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
For ennu må synet vente på sin tid; men det haster mot enden og lyver ikke. Om det dryger, så bi efter det! For komme skal det, det skal ikke utebli.
4 “Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
Se, opblåst og uærlig er hans sjel i ham; men den rettferdige skal leve ved sin tro.
5 ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol h7585)
Så er og vinen troløs; en skrytende mann - han skal ikke bli boende i ro, han som har opspilt sitt grådige svelg likesom dødsriket; han er som døden og blir ikke mett, han har sanket til sig alle folk og samlet til sig alle folkeslag. (Sheol h7585)
6 “Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
Skal ikke alle disse synge nidviser og spottesanger om ham, lage gåter om ham og si: Ve den som dynger op ting som ikke hører ham til - hvor lenge? - og som lesser på sig pantegods!
7 Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
Skal de ikke brått reise sig de som skal pine dig, og våkne op de som skal jage dig op, så du blir et rov for dem?
8 Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
For du har plyndret mange folkeslag; således skal alle som blir igjen av folkene, plyndre dig for din blodskyld mot menneskene og for dine voldsverk mot jorden, mot staden og alle dem som bor i den.
9 “Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
Ve den som jager efter skammelig vinning for sitt hus, for å bygge sitt rede i høiden, for å redde sig fra ulykkens hånd!
10 Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
Du har lagt op råd som blir til skam for ditt hus, lagt op råd om å gjøre ende på mange folk og dermed syndet mot dig selv;
11 Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
for stenen i veggen skal skrike, og bjelken i treverket skal svare den.
12 “Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
Ve den som bygger en by med blod og grunnlegger en stad med urett!
13 Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
Se, kommer det ikke fra Herren, hærskarenes Gud, at folkeslag skal arbeide sig trette for ilden, og folkeferd gjøre sig møie for intet?
14 Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
For jorden skal fylles med kunnskap om Herrens herlighet, likesom vannet som dekker havets bunn.
15 “Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
Ve den som gir sin næste å drikke av sin brennende vredes skål, ja drikker dem drukne, for å se på deres blusel!
16 Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
Du blir mettet med skam og ikke med ære; drikk også du og vis din forhud frem! Begeret i Herrens høire hånd skal i sin tid komme til dig, og dyp skam skal skjule din ære.
17 Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
For ditt voldsverk mot Libanon og ødeleggelsen av dyrene, som skremte dem, skal komme over dig for din blodskyld mot menneskene og for dine voldsverk mot jorden, mot staden og alle dem som bor i den.
18 “Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
Hvad gagn gjør et utskåret billede, om enn en mester har skåret det? Eller hvad gagn gjør et støpt billede, en lærer i løgn, om enn dets mester satte sin lit til det da han gjorde målløse avguder?
19 Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
Ve den som sier til en stokk: Våkn op! - til en målløs sten: Stå op! Skulde den være lærer? Den er jo overtrukket med gull og sølv, og det finnes ikke ånd i den.
20 Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.
Men Herren er i sitt hellige tempel; vær stille for hans åsyn, all jorden!

< Habakkuk 2 >