< Habakkuk 2 >
1 Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
Ngizakuma endaweni yami yokulinda, ngizimise enqabeni, ngilinde, ukuze ngibone ukuthi izakuthini kimi, lokuthi ngizaphendula ngithini ekusolweni kwami.
2 Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
INkosi yasingiphendula yathi: Bhala umbono, uwenze ucace phezu kwezibhebhe, ukuze ogijimayo awufunde.
3 Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
Ngoba umbono usezakuba ngowesikhathi esimisiweyo; kodwa uzakhuluma ekucineni, ungaqambi amanga; lanxa uphuza, uwulindele; ngoba isibili uzafika, kawuyikuphuza.
4 “Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
Khangela, uzikhukhumeza, umphefumulo wakhe kawuqondanga kuye; kodwa olungileyo uzaphila ngokholo lwakhe.
5 ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol )
Yebo futhi, ngoba ekhohlisa ngewayini, engumuntu ozikhukhumezayo, engahlali ekhaya, ekhulisa isiloyiso sakhe njengesihogo, futhi unjengokufa, kasuthiseki, kodwa ubuthelela kuye zonke izizwe, aziqoqele bonke abantu. (Sheol )
6 “Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
Bonke laba kabayikuphakamisa umzekeliso ngaye yini, lesaga esiyinhlekisa ngaye? Njalo bazakuthi: Maye kuye owandisa okungeyisikho okwakhe! Koze kube nini? Lozethwesa ngezibambiso.
7 Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
Kabayikuhle basukume bakulume yini, bavuke abazakuthuthumelisa yini? Njalo uzakuba yizimpango kubo.
8 Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
Ngoba wena uziphangile izizwe ezinengi, yonke insali yabantu izakuphanga; ngenxa yegazi elinengi labantu, lodlakela lwelizwe, umuzi, labo bonke abahlala kiwo.
9 “Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
Maye kozuzela indlu yakhe inzuzo embi, ukuze abeke isidleke sakhe ngaphezulu, ukuze akhululwe esandleni sobubi.
10 Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
Indlu yakho usuyicebele ihlazo, ngokuquma abantu abanengi; wonile umelene lomphefumulo wakho.
11 Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
Ngoba ilitshe lizakhala lisemdulini, lothungo luliphendule lusesigodweni.
12 “Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
Maye kowakha umuzi ngegazi elinengi, amise idolobho ngesiphambeko.
13 Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
Khangela, kakuveli eNkosini yamabandla yini ukuthi izizwe zizatshikatshikela umlilo, labantu bazidinise ngeze?
14 Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
Ngoba umhlaba uzagcwala ngolwazi lwenkazimulo yeNkosi, njengamanzi esibekela ulwandle.
15 “Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
Maye konathisa umakhelwane wakhe, othulula imbodlela yakho, omdakisa laye, ukuze ubukele ubunqunu babo!
16 Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
Uzasutha ngehlazo kulodumo; natha lawe, wembule ijwabu laphambili! Inkezo yesandla seNkosi sokunene izaphendukela kuwe, lehlazo libe phezu kodumo lwakho.
17 Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
Ngoba udlakela lweLebhanoni luzakusibekela, lokuchitheka kwezinyamazana kubethuse, ngenxa yegazi elinengi labantu, lodlakela lwelizwe, umuzi, labo bonke abahlala kiwo.
18 “Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
Sisizani isithombe esibaziweyo lokhu umbumbi waso esibazile? Kumbe isithombe esibunjwe ngokuncibilikisa, lomfundisi wamanga, ukuthi umbumbi athembe kokubunjiweyo kwakhe, ukwenza izithombe eziyizimungulu?
19 Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
Maye kuye otsho kuso isigodo: Phaphama! Lelitsheni eliyisimungulu: Vuka, lona lizafundisa! Khangela, kunanyekwe ngegolide lesiliva, njalo kungekho moya phakathi kwakho.
20 Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.
Kodwa iNkosi isethempelini layo elingcwele; thula phambi kwayo, mhlaba wonke.