< Habakkuk 2 >

1 Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
Je me tiendrai à mon poste et j’arrêterai mes pas sur la fortification, et je regarderai attentivement, afin que je voie ce qui me sera dit, et ce que je répondrai à celui qui m’interpellera.
2 Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
Et le Seigneur me répondit et dit: Écris la vision, et expose-la sur des tablettes, afin que ne s’arrête pas celui qui la lira;
3 Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
Parce que l’accomplissement de la vision est encore éloigné, mais il paraîtra à la fin, et il ne trompera pas, s’il met un certain délai, attends-le; car il va venir, et il ne tardera pas.
4 “Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
Voici que celui qui est incrédule n’aura pas en lui une âme droite; mais le juste vivra de sa foi.
5 ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol h7585)
Et comme le vin trompe celui qui en boit, ainsi en sera-t-il de l’homme superbe, et il ne sera pas honoré; lui qui a dilaté son (Sheol h7585)
6 “Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
Est-ce que tous ceux-ci ne le prendront pas pour un sujet de parabole, et pour le mot de leurs énigmes sur lui, et ne dira-t-on pas: Malheur à celui qui multiplie des biens qui ne sont pas à lui? jusques à quand accumulera-t-il contre lui-même une boue épaisse?
7 Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
Est-ce qu’ils ne se lèveront pas soudain, ceux qui doivent te mordre; et ne se réveilleront-ils pas, ceux qui doivent te déchirer, et ne seras-tu pas leur proie?
8 Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
Parce que tu as dépouillé beaucoup de nations, ils te dépouilleront toi-même, tous ceux qui seront restés des peuples, à cause du sang d’homme que tu as versé, et de l’iniquité que tu as commise sur le pays, la cité et tous ceux qui habitent en elle.
9 “Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
Malheur à qui ramasse les fruits d’une avarice criminelle pour sa maison, afin que son nid soit sur un lieu élevé, et qui pense échapper à la main du malheur.
10 Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
Tu as formé pour ta maison des desseins qui ont été sa confusion, tu as mis en pièces beaucoup de peuples, et ton âme a péché.
11 Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
Parce que la pierre du milieu de la muraille criera; et le bois qui forme les jointures des édifices répondra.
12 “Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
Malheur à celui qui bâtit une cité dans le sang, et qui fonde une ville sur l’iniquité.
13 Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
Est-ce que toutes ces choses ne viennent pas du Seigneur des armées? car des peuples travailleront pour un grand feu, et des nations pour le néant, et périront.
14 Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
Parce que la terre, afin qu’on connaisse la gloire du Seigneur, sera remplie d’ennemis, comme le lit de la mer est couvert par les eaux.
15 “Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
Malheur à celui qui donne à boire à son ami en mettant son fiel dans la coupe et en l’enivrant, afin de regarder sa nudité.
16 Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
Tu as été rempli d’ignominie au lieu de gloire; bois, toi aussi, et sois frappé d’assoupissement; le calice de la droite du Seigneur t’environnera, et un vomissement d’ignominie viendra sur ta gloire.
17 Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
Parce que l’iniquité commise sur le Liban te couvrira, et le ravage exercé sur les animaux les épouvantera à cause du sang les hommes versé, et de l’iniquité commise sur le pays et la cité, et tous ceux qui habitent en elle.
18 “Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
À quoi sert une image taillée au ciseau, que son auteur a faite ainsi qu’une statue jetée en fonte et une image fausse? Car l’auteur a espéré assez dans son œuvre pour faire des simulacres muets.
19 Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
Malheur à celui qui dit au bois: Réveille-toi, à la pierre silencieuse: Lève-toi; est-ce qu’elle-même pourra l’instruire? Voici qu’elle est couverte d’or et d’argent; et il n’y a aucune vie dans ses entrailles.
20 Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.
Mais le Seigneur est dans son temple saint; que devant sa face toute la terre soit en silence.

< Habakkuk 2 >