< Habakkuk 2 >

1 Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
On my kepyng Y schal stonde, and schal pitche a grees on wardyng; and Y schal biholde, that Y se what thing schal be seid to me, and what Y schal answere to hym that repreuith me.
2 Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
And the Lord answeride to me, and seide, Write thou the reuelacioun, and make it pleyn on tablis, that he renne, that schal rede it.
3 Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
For yit the visioun is fer, and it schal appere in to ende, and schal not lie; if it schal make dwellyng, abide thou it, for it comynge schal come, and schal not tarie.
4 “Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
Lo! the soule of hym, that is vnbileueful, schal not be riytful in hym silf; forsothe the iust man schal lyue in his feith.
5 ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol h7585)
And as wyn disseyueth a man drynkynge, so schal the proude man be, and he schal not be maad feir; for as helle he alargide his soule, and he is as deth, and he is not fillid; and he schal gadere to hym alle folkis, and he shal kepe togidere to hym alle puplis. (Sheol h7585)
6 “Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
Whether not alle these puplis schulen take a parable on hym, and the speking of derk sentencis of hym? And it schal be seid, Wo to hym that multiplieth thingis not his owne; hou longe, and he aggreggith ayens hym silf thicke clei?
7 Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
Whether not sudeynli thei schulen rise to gidere, that schulen bite thee? And thei schulen be reisid to-teerynge thee, and thou schalt be in to raueyn to hem; and thin aspieris in yuel schulen wake.
8 Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
For thou robbidist many folkis, alle schulen robbe thee, whiche schulen be left of puplis, for blood of man, and for wickidnesse of lond of the citee, and of alle men dwellynge in it.
9 “Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
Wo to hym that gaderith yuel coueitise to his hous, that his nest be in hiy, and gessith hym for to be delyuered of the hond of yuel.
10 Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
Thou thouytist confusioun to thin hous; thou hast slayn many puplis, and thi soule synnede.
11 Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
For a stoon of the wal schal crie, and a tree that is bitwixe ioynturis of bildyngis schal answere.
12 “Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
Wo to hym that bildith a citee in bloodis, and makith redi a citee in wickidnesse.
13 Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
Whether not these thingis ben of the Lord of oostis? For puplis schulen trauele in myche fier, and folkis in veyn, and thei schulen faile.
14 Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
For the erthe schal be fillid, that it knowe the glorie of the Lord, as watris hilynge the see.
15 “Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
Wo to hym that yyueth drynk to his frend, and sendith his galle, and makith drunkun, that he biholde his nakidnesse.
16 Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
He is fillid with yuel fame for glorie; and thou drynke, and be aslept; the cuppe of the riythalf of the Lord schal cumpasse thee, and `castynge vp of yuel fame on thi glorie.
17 Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
For the wickidnesse of Liban schal kyuere thee, and distruccioun of beestis schal make hem aferd, of bloodis of man, and of wickidnesse of lond, and of the citee, and of alle men dwellynge ther ynne.
18 “Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
What profitith the `grauun ymage, for his makere grauyde it, a wellid thing togidere and fals ymage? for the makere therof hopide in makyng, that he made doumbe symylacris.
19 Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
Wo to hym that seith to a tre, Wake thou; Rise thou, to a stoon beynge stille; whether he schal mow teche? Lo! this is kyuerid with gold and siluer, and no spirit is in his entrails.
20 Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.
Forsothe the Lord is in his hooli temple, al erthe be stille fro his face.

< Habakkuk 2 >