< Habakkuk 2 >
1 Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
I will stand at my guard post and station myself on the watchtower, and I will watch carefully to see what he will say to me and how I should turn from my complaint.
2 Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
Yahweh answered me and said, “Record this vision, and write plainly on the tablets so that the one reading them might run.
3 Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
For the vision is yet for a future time and will finally speak and not fail. Though it delays, wait for it. For it will surely come and will not tarry.
4 “Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
Look! The one whose desires are not right within him is puffed up. But the righteous will live by his faith.
5 ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol )
For wine is a betrayer of the arrogant young man so that he will not abide, but enlarges his desire like the grave and, like death, is never satisfied. He gathers to himself every nation and gathers up for himself all of the peoples. (Sheol )
6 “Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
Will not all these create a saying to ridicule him and a taunting song about him, saying, 'Woe to the one increasing what is not his! For how long will you increase the weight of the pledges you have taken?'
7 Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
Will the ones biting at you not rise up suddenly, and the ones terrifying you awaken? You will become a victim for them.
8 Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
Because you have plundered many peoples, all the remnant of the peoples will plunder you. For you have shed human blood and acted with violence against the land, the cities, and all who live in them.
9 “Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
'Woe to the one who carves out evil gains for his house, so he can set his nest on high to keep himself safe from the hand of evil.'
10 Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
You have devised shame for your house by cutting off many people, and have sinned against yourself.
11 Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
For the stones will cry out from the wall, and the rafters of timber will answer them,
12 “Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
'Woe to the one who builds a city with blood, and who establishes a town in iniquity.'
13 Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
Is it not from Yahweh of hosts that peoples labor for fire and all the other nations weary themselves for nothing?
14 Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
Yet the land will be filled with the knowledge of the glory of Yahweh as the waters cover the sea.
15 “Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
'Woe to the one who forces his neighbors to drink— you express your anger over and you make them drunk in order to look at their nakedness.'
16 Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
You will be filled with shame instead of glory. Now it is your turn! Drink, and you will expose your uncircumcised foreskin! The cup in Yahweh's right hand is coming around to you, and disgrace will cover your glory.
17 Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
The violence done to Lebanon will overwhelm you and the destruction of animals will terrify you. For you have shed human blood and you have acted with violence against the land, the cities, and all who live in them.
18 “Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
What does the carved figure profit you? For the one who has carved it, or who casts a figure from molten metal, is a teacher of lies; for he trusts his own handiwork when he makes these mute gods.
19 Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
'Woe to the one saying to the wood, Wake up! Or to the silent stone, Arise!' Do these things teach? See, it is overlaid with gold and silver, but there is no breath at all within it.
20 Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.
But Yahweh is in his holy temple! Be silent before him, all the land.”