< Habakkuk 1 >
1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
Detta är den tunge, som Propheten Habacuc sett hafver.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
Herre, huru länge skall jag ropa, och du vill icke höra? Huru länge skall jag ropa till dig för öfvervålds skull, och du vill icke hjelpa?
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Hvi låter du mig se mödo och arbete? Hvi hafver du låtit mig se rof och öfvervåld? Våld går öfver rätt.
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
Derföre måste lagen blifva tillbaka, och ingen rätt kan till ända komma; ty den ogudaktige öfverfaller den rättfärdiga, derföre gå vrånga domar.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
Ser ibland Hedningarna; ser till, och förundrer eder ty jag vill något göra i edrom tid, det i icke tro skolen, då man derom talar.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
Ty si, jag vill uppväcka de Chaldeer, ett bittert och snart folk, hvilket draga skall så vidt som landet är, till att intaga de boningar som icke äro deras.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
Och skall vara grufveligit och förfärligit; och skall bjuda och tvinga såsom det vill.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
Deras hästar äro raskare än parder, så äro de ock ilsknare än ulfvar om aftonen; hans resenärer draga med storom hopom fjerranefter, lika som de flögo, såsom örnar hasta sig till ett as.
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
De komma allesamman till att göra skada ehvart de vilja; der gå de igenom, lika som ett östan väder, och samka fångar tillhopa, såsom sand.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
De skola bespotta Konungar, och begabba Förstar; all fäste skola vara dem ett skämt; ty de skola göra der blåverk före, och vinna dem.
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Då skola de taga sig ett nytt mod, fara framåt och synda; och så måste då deras seger höra deras gud till.
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Men du Herre, min Gud, min Helige, du som äst af evighet, låt oss icke dö; utan låt dem, Herre, allenast vara oss till ett straff; och låt dem, o vår tröst, allenast tukta oss.
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Din ögon äro ren, så att du icke orkar se det onda, och kan icke se uppå jämmer. Hvi ser du då på de öfverträdare, och tiger, att den ogudaktige uppslukar den, som frommare är än han?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
Och låter menniskorna gå, lika som fiskar i hafvet; såsom matkar, de ingen herm hafva?
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
De dragat allt med krok, och fuskar med sin nät, och församlat med sin garn; dess fröjda de sig, och äro glade.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
Derföre offra de sinom nätom, och röka sinom garnom; efter det deras del är derigenom så fet, och deras mat så kräselig vorden.
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
Derföre kasta de sin nät ännu alltid ut, och vilja icke återvända att dräpa folk.