< Habakkuk 1 >

1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
The prophecy which Habakkuk the prophet foresaw.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
How long, O Lord, have I entreated [thee], and thou wouldst not hear? [how long] shall I cry out unto thee [because of] violence, and thou wilt not save?
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Why wilt thou let me see wickedness, and wilt look on trouble, and the robbery and violence [that are] before me: while there is strife, and contention lifteth up [its head]?
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
Therefore is the law powerless, and justice cometh not forth victorious; for the wicked encompasseth about the righteous; therefore doth justice come forth perverted.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
Look ye about among the nations, and behold and be astonished and astounded; for [God] will fulfill a work in your days, ye would not believe it, if it were only told you.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
For, lo, I will raise up the Chaldeans, that bitter and impetuous nation, that march to the wide spaces of the earth to conquer dwelling-places that are not theirs.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
Terrible and dreadful are they: from themselves go forth their judicial laws and their dignity.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
And swifter than leopards are their horses, and fiercer than the evening wolves; and their horsemen spread themselves abroad: and their horsemen will come from afar; they will fly like the eagle hastening to eat.
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
They all will come for violence: the front of their faces is like the east wind, and they gather captives as the sand.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
And they will make sport with kings, and princes will be a play unto them: at every strong-hold will they laugh, and they will cast up earth-mounds and capture it.
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Then doth their spirit become arrogant, and they are surpassingly proud, and offend, [imputing] this their power unto their god.
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Art thou not from everlasting, O Lord my God, my Holy One? we shall not die. O Lord, thou hast ordained them for judgment; and, O Protector, thou hast appointed them to correct [nations].
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Thou, who art too pure of eyes to behold evil, and canst not look on trouble, wherefore wilt thou look upon those that deal treacherously, be silent when the wicked swalloweth up him that is more righteous than he?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
And [why] makest thou men as the fishes of the sea, as the creeping things, that have no ruler over them?
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
All of them he bringeth up with the angle, he draggeth them up in his net, and gathereth them in his drag: therefore he rejoiceth and is glad.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
Therefore he sacrificeth unto his net, and burneth incense unto his drag; because through them is his portion fat, and his food marrowy.
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
Shall he therefore [always] empty his net, and continually slay nations without sparing?

< Habakkuk 1 >