+ Farawa 1 >

1 A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
Long, long ago God created the heavens and the earth.
2 To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
When he began to create the earth, it was shapeless and completely desolate/chaotic. Darkness covered the deep water that surrounded the earth. And the Spirit of God was hovering over the water.
3 Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
God said, “I want light to shine!” And light shone.
4 Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
God was pleased with the light. Then he made the light to shine in some places, and in other places there was still darkness.
5 Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
He gave to the light the name ‘day’, and he gave to the darkness the name ‘night’. After that, there was an evening which was followed by a morning. He called that whole period of time ‘the first day’.
6 Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
Then God said, “I command that there be an empty space like a huge dome to separate the water that is above it from the water on the earth that is below it!”
7 Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
And that is what happened. God gave to the space the name ‘sky’.
8 Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
Then there was another evening, which was followed by another morning. He called that period of time ‘the second day’.
9 Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
Then God said, “I want the water that is below the sky to come together, and dry ground to appear and rise above the water.” And that is what happened.
10 Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
God gave to the ground the name ‘earth’, and he gave to the water that came together the name ‘oceans’. God was pleased with the earth and the oceans.
11 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
Then God said, “I want the earth to produce plants, including plants that will produce seeds and trees that will produce fruit. Each kind of tree will bear its own kind of fruit.”
12 Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
Then plants grew on the earth; each kind of plant began to produce its own kind of seed.
13 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
Then there was another evening which was followed by another morning. God called that period of time ‘the third day’.
14 Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
Then God said, “I want a sun, a moon, and many stars to shine in the sky. The sun will shine in the daytime and the moon and stars will shine during the nighttime. By the changes in their appearance they will indicate the various seasons (OR, the times for special celebrations), and will enable people to know when days and years begin.
15 bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
I want them also to be like lights in the sky that will shine on the earth.” And that is what happened.
16 Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
God made two of them that were like big lights. The bigger one, the sun, shines during the day and the smaller one, the moon, shines during the night. He also made the stars.
17 Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
God set all of them in the sky to shine on the earth,
18 su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
to rule the day and the night, and to separate the light of the daytime from the darkness of the nighttime. God was pleased with these things he had made.
19 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
Then there was another evening which was followed by another morning. He called that period of time ‘the fourth day’.
20 Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
Then God said, “I want many creatures to live in all the oceans, and I also want birds to fly in the sky above the earth.”
21 Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
So God created huge sea creatures and every other kind of creature that moves in the water, and caused them to live in all the oceans. He also created many kinds of birds. God was pleased with all those creatures.
22 Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
God blessed them. He said, “Produce offspring and become very numerous. I want the creatures in the water to live in all the oceans, and birds also to become very numerous.” And that is what happened.
23 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
Then there was another evening that was followed by another morning. He called that period of time ‘the fifth day’.
24 Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
Then God said, “I want various kinds of creatures to appear on the earth. There will be many kinds of (livestock/domestic animals), creatures that scurry across the ground, and large wild animals.” And that is what happened.
25 Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
God made all kinds of wild animals and (livestock/domestic animals) and all kinds of creatures that scurry across the ground. God was pleased with all these creatures.
26 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
Then God said, “Now we will make human beings that will be like us in many ways. I want them to rule over the fish in the sea, over the birds, over all the (livestock/domestic animals), and over all the other creatures that scurry across the ground.”
27 Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
So God created human beings that were like him in many ways. He made them to be like himself. He created some to be male and some to be female.
28 Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
God blessed them, saying, “Produce many children, who will live all over the earth and rule over it. I want them to rule over the fish and the birds and over all creatures that scurry across the ground.”
29 Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
God said to the humans, “Listen! I have given you all the plants that produce seeds, all over the earth, and all the trees that have seeds in their fruit. All these things are for you to eat.
30 Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
I have given all the green plants to all the wild animals and to the birds and to all the creatures that scurry across the ground, to everything that breathes, for them to eat.” And that is what happened.
31 Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.
God was pleased with everything that he had made. Truly, it was all very good. Then there was another evening, that was followed by another morning. He called that period of time ‘the sixth day’.

+ Farawa 1 >