< Farawa 9 >

1 Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
Et Dieu bénit Noé et ses fils, et leur dit: Fructifiez et multipliez et remplissez la terre.
2 Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
Et vous serez un sujet de crainte et de frayeur pour tout animal de la terre, et pour tout oiseau des cieux, pour tout ce qui se meut sur la terre, aussi bien que pour tous les poissons de la mer; ils sont livrés entre vos mains.
3 Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
Tout ce qui se meut [et] qui est vivant vous sera pour nourriture; comme l’herbe verte, je vous donne tout.
4 “Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
Seulement, vous ne mangerez pas la chair avec sa vie, [c’est-à-dire] son sang;
5 Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
et certes je redemanderai le sang de vos vies; de la main de tout animal je le redemanderai, et de la main de l’homme; de la main de chacun, de son frère, je redemanderai la vie de l’homme.
6 “Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
Qui aura versé le sang de l’homme, par l’homme son sang sera versé; car à l’image de Dieu, il a fait l’homme.
7 Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
Et vous, fructifiez et multipliez; foisonnez sur la terre, et multipliez sur elle.
8 Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
Et Dieu parla à Noé et à ses fils avec lui, disant:
9 “Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
Et moi, voici, j’établis mon alliance avec vous, et avec votre semence après vous,
10 da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
et avec tout être vivant qui est avec vous, tant oiseaux que bétail et tout animal de la terre avec vous, d’entre tout ce qui est sorti de l’arche, – tout animal de la terre.
11 Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
Et j’établis mon alliance avec vous, et toute chair ne périra plus par les eaux du déluge, et il n’y aura plus de déluge pour détruire la terre.
12 Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
Et Dieu dit: C’est ici le signe de l’alliance que je mets entre moi et vous et tout être vivant qui est avec vous, pour les générations, à toujours:
13 Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
je mettrai mon arc dans la nuée, et il sera pour signe d’alliance entre moi et la terre;
14 Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
et il arrivera que quand je ferai venir des nuages sur la terre, alors l’arc apparaîtra dans la nuée,
15 zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
et je me souviendrai de mon alliance qui est entre moi et vous et tout être vivant de toute chair; et les eaux ne deviendront plus un déluge pour détruire toute chair.
16 Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
Et l’arc sera dans la nuée, et je le verrai pour me souvenir de l’alliance perpétuelle entre Dieu et tout être vivant de toute chair qui est sur la terre.
17 Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
Et Dieu dit à Noé: C’est là le signe de l’alliance que j’établis entre moi et toute chair qui est sur la terre.
18 ’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
Et les fils de Noé qui sortirent de l’arche étaient Sem, et Cham, et Japheth: et Cham fut le père de Canaan.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
Ces trois sont fils de Noé; et c’est d’eux que la population fut disséminée sur toute la terre.
20 Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
Et Noé commença à être cultivateur et il planta une vigne;
21 Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
et il but du vin, et il s’enivra et se découvrit au milieu de la tente.
22 Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
Et Cham, père de Canaan, vit la nudité de son père, et le rapporta à ses deux frères, dehors.
23 Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
Et Sem et Japheth prirent le manteau et le mirent, les deux, sur leurs épaules et marchèrent en arrière et couvrirent la nudité de leur père; et leur visage était [tourné] en arrière, et ils ne virent pas la nudité de leur père.
24 Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
Et Noé se réveilla de son vin et sut ce que lui avait fait son plus jeune fils;
25 sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
et il dit: Maudit soit Canaan! Il sera l’esclave des esclaves de ses frères.
26 Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
Et il dit: Béni soit l’Éternel, le Dieu de Sem, et que Canaan soit son esclave!
27 Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
Que Dieu élargisse Japheth, et qu’il demeure dans les tentes de Sem, et que Canaan soit son esclave!
28 Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
Et Noé vécut, après le déluge, 350 ans.
29 Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.
Et tous les jours de Noé furent 950 ans; et il mourut.

< Farawa 9 >