< Farawa 9 >

1 Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
And God gave his blessing to Noah and his sons, and said, Be fertile, and have increase, and make the earth full.
2 Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
And the fear of you will be strong in every beast of the earth and every bird of the air; everything which goes on the land, and all the fishes of the sea, are given into your hands.
3 Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
Every living and moving thing will be food for you; I give them all to you as before I gave you all green things.
4 “Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
But flesh with the life-blood in it you may not take for food.
5 Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
And for your blood, which is your life, will I take payment; from every beast I will take it, and from every man will I take payment for the blood of his brother-man.
6 “Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
Whoever takes a man's life, by man will his life be taken; because God made man in his image.
7 Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
And now, be fertile and have increase; have offspring on the earth and become great in number.
8 Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
And God said to Noah and to his sons,
9 “Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
Truly, I will make my agreement with you and with your seed after you,
10 da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
And with every living thing with you, all birds and cattle and every beast of the earth which comes out of the ark with you.
11 Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
And I will make my agreement with you; never again will all flesh be cut off by the waters; never again will the waters come over all the earth for its destruction.
12 Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
And God said, This is the sign of the agreement which I make between me and you and every living thing with you, for all future generations:
13 Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
I will put my bow in the cloud and it will be for a sign of the agreement between me and the earth.
14 Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
And whenever I make a cloud come over the earth, the bow will be seen in the cloud,
15 zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
And I will keep in mind the agreement between me and you and every living thing; and never again will there be a great flow of waters causing destruction to all flesh.
16 Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
And the bow will be in the cloud, and looking on it, I will keep in mind the eternal agreement between God and every living thing on the earth.
17 Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
And God said to Noah, This is the sign of the agreement which I have made between me and all flesh on the earth.
18 ’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
And the sons of Noah who went out of the ark were Shem, Ham, and Japheth; and Ham is the father of Canaan.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
These three were the sons of Noah and from them all the earth was peopled.
20 Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
In those days Noah became a farmer, and he made a vine-garden.
21 Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
And he took of the wine of it and was overcome by drink; and he was uncovered in his tent.
22 Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
And Ham, the father of Canaan, saw his father unclothed, and gave news of it to his two brothers outside.
23 Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
And Shem and Japheth took a robe, and putting it on their backs went in with their faces turned away, and put it over their father so that they might not see him unclothed.
24 Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
And, awaking from his wine, Noah saw what his youngest son had done to him, and he said,
25 sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
Cursed be Canaan; let him be a servant of servants to his brothers.
26 Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
And he said, Praise to the Lord, the God of Shem; let Canaan be his servant.
27 Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
May God make Japheth great, and let his living-place be in the tents of Shem, and let Canaan be his servant.
28 Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
And Noah went on living three hundred and fifty years after the great flow of waters;
29 Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.
all the years of his life were nine hundred and fifty: and he came to his end.

< Farawa 9 >