< Farawa 8 >

1 Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
A Bog se opomenu Noja i svijeh zvijeri i sve stoke što bjehu s njim u kovèegu; i posla Bog vjetar na zemlju da uzbije vodu.
2 Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
I zatvoriše se izvori bezdanu i ustave nebeske, i dažd s neba prestade.
3 Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
I stade voda opadati na zemlji, i jednako opadaše poslije sto i pedeset dana;
4 A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
Te se ustavi kovèeg sedmoga mjeseca dana sedamnaestoga na planini Araratu.
5 Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
I voda opadaše sve veæma do desetoga mjeseca; i prvoga dana desetoga mjeseca pokazaše se vrhovi od brda.
6 Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
A poslije èetrdeset dana otvori Noje prozor na kovèegu, koji bješe naèinio;
7 ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
I ispusti gavrana, koji jednako odlijetaše i dolijetaše dokle ne presahnu voda na zemlji.
8 Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
Pa pusti i golubicu da bi vidio je li opala voda sa zemlje.
9 Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
A golubica ne našavši gdje bi stala nogom svojom vrati se k njemu u kovèeg, jer još bješe voda po svoj zemlji; i Noje pruživši ruku uhvati je i uze k sebi u kovèeg.
10 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
I poèeka još sedam dana, pa opet ispusti golubicu iz kovèega.
11 Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
I pred veèe vrati se k njemu golubica, i gle, u kljunu joj list maslinov, koji bješe otkinula; tako pozna Noje da je opala voda sa zemlje.
12 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
Ali poèeka još sedam dana, pa opet ispusti golubicu, a ona mu se više ne vrati.
13 A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
Šest stotina prve godine vijeka Nojeva prvi dan prvoga mjeseca usahnu voda na zemlji; i Noje otkri krov na kovèegu, i ugleda zemlju suhu.
14 A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
A drugoga mjeseca dvadeset sedmoga dana bješe sva zemlja suha.
15 Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
Tada reèe Bog Noju govoreæi:
16 “Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
Izidi iz kovèega ti i žena tvoja i sinovi tvoji i žene sinova tvojih s tobom;
17 Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
Sve zvijeri što su s tobom od svakoga tijela, ptice i stoku i što god gamiže po zemlji, izvedi sa sobom, neka se raziðu po zemlji, i neka se plode i množe na zemlji.
18 Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
I izide Noje i sinovi njegovi i žena njegova i žene sinova njegovijeh s njim.
19 da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
Sve zvijeri, sve sitne životinje, sve ptice i sve što se mièe po zemlji po svojim vrstama izidoše iz kovèega.
20 Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
I naèini Noje žrtvenik Gospodu, i uze od svake èiste stoke i od svijeh ptica èistijeh, i prinese na žrtveniku žrtve paljenice.
21 Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
I Gospod omirisa miris ugodni, i reèe u srcu svojem: neæu više kleti zemlje s ljudi, što je misao srca èovjeèijega zla od malena; niti æu više ubijati svega što živi, kao što uèinih.
22 “Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”
Otsele dokle bude zemlje, neæe nestajati sjetve ni žetve, studeni ni vruæine, ljeta ni zime, dana ni noæi.

< Farawa 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark