< Farawa 8 >

1 Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
Et Dieu se souvint de Noé, et de tous les animaux et de tout le bétail, qui étaient avec lui dans l’arche; et Dieu fit passer un vent sur la terre, et les eaux baissèrent;
2 Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
et les fontaines de l’abîme et les écluses des cieux furent fermées, et la pluie qui tombait du ciel fut retenue.
3 Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
Et les eaux se retirèrent de dessus la terre, allant et se retirant; et les eaux diminuèrent au bout de 150 jours.
4 A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
Et l’arche reposa sur les montagnes d’Ararat, au septième mois, au dix-septième jour du mois.
5 Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
Et les eaux allèrent diminuant jusqu’au dixième mois; au dixième [mois], le premier [jour] du mois, les sommets des montagnes apparurent.
6 Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
Et il arriva, au bout de 40 jours, que Noé ouvrit la fenêtre de l’arche qu’il avait faite;
7 ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
et il lâcha le corbeau, qui sortit, allant et revenant jusqu’à ce que les eaux aient séché de dessus la terre.
8 Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
Et il lâcha d’avec lui la colombe, pour voir si les eaux avaient baissé sur la face du sol;
9 Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
mais la colombe ne trouva pas où poser la plante de son pied, et revint à lui dans l’arche, car les eaux étaient sur la face de toute la terre; et il étendit sa main, et la prit, et la fit entrer auprès de lui dans l’arche.
10 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
Et il attendit encore sept autres jours, et il lâcha de nouveau la colombe hors de l’arche.
11 Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
Et la colombe vint à lui au temps du soir, et voici, dans son bec, une feuille d’olivier arrachée. Et Noé sut que les eaux avaient baissé sur la terre.
12 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
Et il attendit encore sept autres jours, et il lâcha la colombe, et elle ne revint plus de nouveau vers lui.
13 A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
Et il arriva, l’an 601, au premier [mois], le premier [jour] du mois, que les eaux furent séchées de dessus la terre; et Noé ôta la couverture de l’arche et regarda, et voici, la face du sol avait séché.
14 A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
Et au second mois, le vingt-septième jour du mois, la terre fut sèche.
15 Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
Et Dieu parla à Noé, disant:
16 “Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
Sors de l’arche, toi, et ta femme et tes fils et les femmes de tes fils avec toi.
17 Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
Fais sortir avec toi tout animal qui est avec toi, de toute chair, tant oiseaux que bétail, et tout reptile qui rampe sur la terre, et qu’ils foisonnent en la terre, et fructifient et multiplient sur la terre.
18 Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
Et Noé sortit, et ses fils, et sa femme et les femmes de ses fils avec lui.
19 da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
Tout animal, tout reptile et tout oiseau, tout ce qui se meut sur la terre, selon leurs espèces, sortirent de l’arche.
20 Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
Et Noé bâtit un autel à l’Éternel, et prit de toute bête pure et de tout oiseau pur, et offrit des holocaustes sur l’autel.
21 Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
Et l’Éternel flaira une odeur agréable; et l’Éternel dit en son cœur: Je ne maudirai plus de nouveau le sol à cause de l’homme, car l’imagination du cœur de l’homme est mauvaise dès sa jeunesse; et je ne frapperai plus de nouveau tout ce qui est vivant, comme je l’ai fait.
22 “Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”
Désormais, tant que seront les jours de la terre, les semailles et la moisson, et le froid et le chaud, et l’été et l’hiver, et le jour et la nuit, ne cesseront pas.

< Farawa 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark