< Farawa 8 >
1 Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
And God remembered Noah, and all the wild—beasts and all the tame-beasts that were with him in the ark, —and God caused a wind to pass over the earth, and the waters subsided;
2 Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
and the fountains of the roaring-deep were shut, and the windows of the heavens, —and the heavy rain was restrained from the heavens;
3 Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
and the waters returned from off the earth they went on returning, —and so the waters decreased at the end of a hundred and fifty days.
4 A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
And the ark rested, in the seventh month, on the seventeenth day of the month, —on the mountains of Ararat.
5 Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
But, the waters went on decreasing, until the tenth month, —in the tenth [month], on the first of the month, were seen the tops of the mountains.
6 Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
And it came to pass at the end of forty days, that Noah opened the window of the ark that he had made;
7 ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
and sent forth a raven, —and it kept going forth and returning, until the drying up of the waters from off the earth.
8 Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
And he sent forth a dove from him, —to see whether the waters had abated, from off the face of the ground;
9 Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
but the dove found no resting-place for the sole of her foot so she returned unto him into the ark, for, waters, were on the face of all the earth; and he put forth his hand and took her, and brought her in unto him, into the ark.
10 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
Then stayed he yet seven days more, —and, again sent forth the dove out of the ark.
11 Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
And the dove came in unto him at eventide, and lo! a newly sprouted olive-leaf, in her mouth, —so Noah knew that the waters had abated from off the earth.
12 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
And he stayed yet seven days more, —and sent forth the dove, but she returned not again unto him any more.
13 A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
So it came to pass in the six hundred and first year at the beginning, on the first of the month, that the waters had dried up from off the earth, —and Noah removed the covering of the ark, and looked and lo! the face of the ground was dried.
14 A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
And in the second month, on the twenty-seventh day of the month, was the earth dry.
15 Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
So then, God spake to Noah, saying:
16 “Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
Come forth out of the ark, —thou and thy wife, and thy sons, and thy sons’ wives with thee.
17 Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
All the living creatures that are with thee of all flesh among birds, and among beasts, and among all the creeping things that creep on the earth, bring forth with thee, —and they shall swarm in the earth, and be fruitful and multiply, on the earth.
18 Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
So Noah came forth, —and his sons and his wife, and his sons’ wives with him:
19 da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
All the living creatures, all that move along, and all birds, and all that moveth along over the earth—by their families, came forth out of the ark.
20 Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
And Noah builded an altar to Yahweh, —and took of all the clean beasts and of all the clean birds, and caused ascending Sacrifices to go up on the altar.
21 Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
And Yahweh smelled a satisfying odour, so Yahweh said to himself. I will not, again, curse any more the ground for man’s sake, although the device of the heart of man, be wicked from his youth, —neither will I again, any more smite every living thing, as I have done.
22 “Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”
During all the days of the earth, seedtime and harvest, and cold and heat and summer and winter, and day and night, shall not cease.