< Farawa 8 >

1 Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
And God remembers Noah, and every living thing, and all the livestock which [are] with him in the Ark, and God causes a wind to pass over the earth, and the waters subside,
2 Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
and the fountains of the deep and the network of the heavens are closed, and the shower is restrained from the heavens.
3 Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
And the waters return from off the earth, going on and returning; and the waters are lacking at the end of one hundred and fifty days.
4 A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
And the Ark rests, in the seventh month, on the seventeenth day of the month, on mountains of Ararat;
5 Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
and the waters have been going and decreasing until the tenth month; in the tenth [month], on the first of the month, the heads of the mountains appeared.
6 Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
And it comes to pass, at the end of forty days, that Noah opens the window of the Ark which he made,
7 ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
and he sends forth the raven, and it goes out, going out and turning back until the drying of the waters from off the earth.
8 Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
And he sends forth the dove from him to see whether the waters have been lightened from off the face of the ground,
9 Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
and the dove has not found rest for the sole of her foot, and she turns back to him, to the Ark, for waters [are] on the face of all the earth, and he puts out his hand, and takes her, and brings her in to him, into the Ark.
10 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
And he stays yet seven more days, and adds to send forth the dove from the Ark;
11 Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
and the dove comes to him at evening, and behold, an olive leaf [is] torn off in her mouth; and Noah knows that the waters have been lightened from off the earth.
12 Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
And he stays yet seven more days, and sends forth the dove, and it did not add to return to him anymore.
13 A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
And it comes to pass in the six hundredth and first year, in the first [month], on the first of the month, the waters have been dried from off the earth; and Noah turns aside the covering of the Ark, and looks, and behold, the face of the ground has been dried.
14 A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
And in the second month, on the twenty-seventh day of the month, the earth has become dry.
15 Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
And God speaks to Noah, saying, “Go out from the Ark, you, and your wife, and your sons, and your sons’ wives with you;
16 “Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
every living thing that [is] with you, of all flesh, among bird, and among livestock, and among every creeping thing which is creeping on the earth, bring out with you;
17 Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
and they have teemed in the earth, and been fruitful, and have multiplied on the earth.”
18 Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
And Noah goes out, and his sons, and his wife, and his sons’ wives with him;
19 da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
every beast, every creeping thing, and every bird; every creeping thing on the earth, after their families, have gone out from the Ark.
20 Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
And Noah builds an altar to YHWH, and takes from every clean beast and from every clean bird, and causes burnt-offerings to ascend on the altar;
21 Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
and YHWH smells the refreshing fragrance, and YHWH says to His heart, “I do not continue to disfavor the ground because of man anymore, though the imagination of the heart of man [is] evil from his youth; and I do not continue to strike all living anymore, as I have done;
22 “Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”
during all [the] days of the earth, seed-time and harvest, and cold and heat, and summer and winter, and day and night never cease.”

< Farawa 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark