< Farawa 7 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
Y él Señor dijo a Noé: Toma a toda tu familia, y entra en el arca; porque solo tu en esta generación he visto que eres recto.
2 Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
De toda bestia limpia tomarás siete machos y siete hembras, y de las bestias que no son limpias, dos, el macho y su hembra;
3 da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
Y de las aves del cielo, siete machos y siete hembras, para que su simiente aún viva sobre la faz de la tierra.
4 Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
Porque después de siete días enviaré lluvia sobre la tierra durante cuarenta días y cuarenta noches, para destrucción de todo ser viviente que hice sobre la faz de la tierra.
5 Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
Y Noé hizo todo lo que el Señor le ordenó.
6 Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
Y Noé tenía seiscientos años cuando las aguas fluían sobre toda la tierra.
7 Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
Y Noé, con sus hijos, su mujer y las mujeres de sus hijos, entró en el arca a causa del fluir de las aguas.
8 Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
De bestias limpias, y de bestias que no son limpias, y de aves, y de todo lo que va sobre la tierra,
9 namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
En parejas, hombres y mujeres, entraron al arca con Noé, como Dios había dicho.
10 Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
Y después de los siete días, las aguas del diluvio pasaron sobre toda la tierra.
11 A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
En el año seiscientos de la vida de Noé, en el mes segundo, a los diecisiete días del mes, todas las fuentes del gran abismo se reventaron, y las ventanas del cielo se abrieron;
12 Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
Y cayó la lluvia sobre la tierra por cuarenta días y cuarenta noches.
13 A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
El mismo día, Noé, con Sem, Cam y Jafet, sus hijos, su mujer y las esposas de sus hijos, entraron en el arca;
14 Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
Y con ellos toda clase de bestias salvajes, y bestias domesticadas, y toda clase de cosas que se arrastran sobre la tierra, y toda clase de aves.
15 Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
Ellos fueron con Noé al arca, dos en dos de toda carne en la cual es el aliento de la vida.
16 Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
Entraron hombres y mujeres de toda carne, como Dios había dicho, y el arca fue cerrada por el Señor.
17 Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
Y por cuarenta días fueron las aguas sobre toda la tierra; y las aguas aumentaron, de modo que el arca se elevó por encima de la tierra.
18 Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
Y las aguas cubrieron todas las cosas, y fueron incrementadas en la tierra, y el arca reposó sobre la faz de las aguas.
19 Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
Y las aguas han vencido a todo lo que hay en la tierra; y todas las montañas debajo del cielo fueron cubiertas.
20 Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
Las aguas subían quince codos, hasta que se cubrieron todas las montañas.
21 Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
Y la destrucción vino sobre todo ser viviente que se movía sobre la tierra, aves, ganado, bestias, y todo lo que había en la tierra, y todo hombre.
22 Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
Todo en la tierra seca, en el cual era el aliento de la vida, llegó a su fin.
23 Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
Todo ser viviente sobre la faz de la tierra, el hombre y el ganado y las cosas que se mueven sobre la faz de la tierra, y las aves del cielo, vinieron a la destrucción; sólo Noé y los que estaban con él en el arca, fueron guardados de la muerte.
24 Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.
Y las aguas sobre la tierra fueron ciento cincuenta días.