< Farawa 7 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
Dieu dit alors à Noé: Entre dans l'arche avec toute ta maison, parce que parmi toute cette race, je t'ai vu juste devant moi.
2 Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
De tous les bestiaux purs introduis auprès de toi sept couples, mâles et femelles, et de tous les animaux impurs deux couples mâles et femelles;
3 da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
De tous les oiseaux purs du ciel sept couples mâles et femelles, et de tous les oiseaux impurs deux couples mâles et femelles, afin d'en conserver la semence pour toute la terre.
4 Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
Car, encore sept jours, et je ferai tomber la pluie sur toute la terre, quarante jours et quarante nuits; et j'effacerai de la face de toute la terre tout ce qui s'y élève et que j'ai fait.
5 Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
Noé fit tout ce que lui ordonna le Seigneur Dieu.
6 Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
Il était âgé de six cents ans, lorsque le déluge vint sur la terre.
7 Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
Bientôt Noé, et avec lui ses fils, et sa femme, et les femmes de ses fils entrèrent dans l'arche, à cause de l'eau du déluge.
8 Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
De tous les oiseaux purs et de tous les oiseaux impurs, de tous les bestiaux puis et de tous les bestiaux impurs, ainsi que de tous les animaux qui rampent sur la terre,
9 namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
Deux couples mâles et femelles entrèrent auprès de Noé dans l'arche, selon que le Seigneur avait prescrit à Noé.
10 Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
Et après que les sept jours furent passés, l'eau du déluge vint sur la terre.
11 A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
L'an six cent de la vie de Noé, le vingt-septième jour de la seconde lune, toutes les sources de l'abîme jaillirent et les cataractes du ciel furent rompues.
12 Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
La pluie tomba sur la terre quarante jours et quarante nuits.
13 A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
En ces jours-là, Noé, Sem, Cham, Japhet, fils de Noé, la femme de Noé et les trois femmes de ses fils, étaient entrés dans l'arche.
14 Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
Et toutes les bêtes fauves, par espèces; tous les bestiaux, par espèces; tous les reptiles se traînant à terre, par espèces; tous les oiseaux ailés, par espèces;
15 Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
Étaient entrés auprès de Noé, dans l'arche, par deux couples, mâles et femelles, de toute chair en laquelle était souffle de vie.
16 Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
Tous les mâles et femelles de toute chair étaient donc entrés dans l'arche, selon ce que le Seigneur avait prescrit à Noé, et le Seigneur Dieu avait fermé l'arche en dehors.
17 Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
Et le déluge fut sur toute la terre quarante jours et quarante nuits; l'eau se gonfla, et emporta l'arche qui s'éleva bien au-dessus de la terre.
18 Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
Et l'eau dominait; elle montait, montait toujours sur la terre, et l'arche était portée sur la surface de l'eau.
19 Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
Et l'eau dominait beaucoup, beaucoup sur la terre; et elle couvrait toutes les hautes montagnes qui étaient sous le ciel.
20 Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
L'eau s'éleva à quinze coudées au-dessus de leur sommet.
21 Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
Alors mourut toute chair se mouvant sur la terre, oiseaux et bestiaux, bêtes fauves et reptiles se traînant à terre, et tout homme.
22 Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
Tout ce qui avait souffle de vie, et tout ce qui vivait sur la terre ferme mourut.
23 Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
L'eau effaça tout ce qui se mouvait sur la face de la terre, depuis l'homme jusqu'aux bestiaux, tous les reptiles, et les oiseaux du ciel. Ils furent tous effacés de la terre. Noé seul resta, et ceux qui étaient dans l'arche avec lui.
24 Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.
L'eau se maintint au-dessus de la terre cent cinquante jours.