< Farawa 7 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
And the Lord said to him: “Enter the ark, you and all your house. For I have seen you to be just in my sight, within this generation.
2 Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
From all the clean animals, take seven and seven, the male and the female. Yet truly, from animals that are unclean, take two and two, the male and the female.
3 da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
But also from the birds of the air, take seven and seven, the male and the female, so that offspring may be saved upon the face of the whole earth.
4 Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
For from that point, and after seven days, I will rain upon the earth for forty days and forty nights. And I will wipe away every substance that I have made, from the surface of the earth.”
5 Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
Therefore, Noah did all things just as the Lord had commanded him.
6 Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
And he was six hundred years old when the waters of the great flood inundated the earth.
7 Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
And Noah entered into the ark, and his sons, his wife, and the wives of his sons with him, because of the waters of the great flood.
8 Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
And from the animals both clean and unclean, and from the birds, and from everything that moves upon the earth,
9 namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
two by two they were brought into the ark to Noah, male and female, just as the Lord had instructed Noah.
10 Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
And when seven days had passed, the waters of the great flood inundated the earth.
11 A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
In the six hundredth year of the life of Noah, in the second month, on the seventeenth day of the month, all the fountains of the great abyss were released, and the floodgates of heaven were opened.
12 Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
And rain came upon the earth for forty days and forty nights.
13 A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
On the very same day, Noah and his sons, Shem, Ham, and Japheth, and his wife and the three wives of his sons with them, entered the ark.
14 Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
They and every animal according to its kind, and all the cattle in their kind, and everything that moves upon the earth in their kind, and every flying thing according to its kind, all the birds and all that can fly,
15 Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
entered the ark to Noah, two by two out of all that is flesh, in which there was the breath of life.
16 Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
And those that entered went in male and female, from all that is flesh, just as God had instructed him. And then the Lord closed him in from the outside.
17 Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
And the great flood occurred for forty days upon the earth. And the waters were increased, and they lifted the ark high above the land.
18 Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
For they overflowed greatly, and they filled everything on the surface of the earth. And then the ark was carried across the waters.
19 Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
And the waters prevailed beyond measure across the earth. And all the lofty mountains under the whole heaven were covered.
20 Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
The water was fifteen cubits higher than the mountains which it covered.
21 Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
And all flesh was consumed which moved upon the earth: flying things, animals, wild beasts, and all moving things that crawl upon the ground. And all men,
22 Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
and everything in which there is the breath of life on earth, died.
23 Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
And he wiped away all substance that was upon the earth, from man to animal, the crawling things just as much as the flying things of the air. And they were wiped away from the earth. But only Noah remained, and those who were with him in the ark.
24 Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.
And the waters possessed the earth for one hundred and fifty days.