< Farawa 7 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
Og Herren sagde til Noa: Gak ind, du og dit ganske Hus, i Arken; thi dig har jeg set retfærdig for mig i denne Slægt.
2 Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
Tag dig af alle Haande rent Kvæg syv og syv, Han og Hun; men af det Kvæg, som er urent, et Par, Han og Hun;
3 da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
ogsaa af Fuglene under Himmelen, syv og syv, Han og Hun, at holde Sæd paa al Jorden i Live.
4 Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
Thi end om syv Dage vil jeg lade regne paa Jorden fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter og udslette af Jorden alle levende Væsener, som jeg har gjort.
5 Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
Og Noa gjorde efter alt, hvad Herren bød ham.
6 Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
Og der Noa var seks Hundrede Aar gammel, da kom Floden med Vande over Jorden.
7 Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
Og Noa gik ind og hans Sønner og hans Hustru og hans Sønners Hustruer med ham i Arken for Flodens Vande.
8 Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
Af rent Kvæg og af det Kvæg, som ikke er rent, og af Fuglene og alt det, som kryber paa Jorden,
9 namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
gik Par og Par til Noa til Arken, Han og Hun, ligesom Gud havde befalet Noa.
10 Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
Og det skete paa den syvende Dag, da kom Flodens Vande over Jorden.
11 A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
I det Aar, der Noa var seks Hundrede Aar gammel, i den anden Maaned, paa den syttende Dag i Maaneden, paa den Dag opbrast alle Kilder i den store Afgrund, og Himmelens Sluser oplodes.
12 Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
Og der var Regn paa Jorden fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter.
13 A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
Paa den selvsamme Dag gik Noa og Sem og Kam og Jafet, Noas Sønner, og Noas Hustru og hans Sønners tre Hustruer med dem i Arken;
14 Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
de og alle Haande vilde Dyr efter deres Slags og alle Haande Kvæg efter deres Slags og alle Haande Kryb, som krybe paa Jorden, efter deres Slags, og alle Haande Fugle efter deres Slags, alt det, som kan flyve, alt det, som har Vinger.
15 Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
Og de gik i Arken til Noa, Par og Par af alt Kød, i hvilket der var Livs Aande.
16 Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
Og de, som kom, kom Han og Hun af alle Haande Kød, ligesom Gud havde budet ham; og Herren lukkede til efter ham.
17 Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
Da kom Floden fyrretyve Dage over Jorden; og Vandet formeredes og opløftede Arken, og den hævedes op over Jorden.
18 Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
Og Vandet fik Overhaand og formeredes saare over Jorden; og Arken flød oven paa Vandet.
19 Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
Og Vandet fik Overhaand saare meget over Jorden; og alle høje Bjerge bleve skjulte, som vare under den ganske Himmel.
20 Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
Femten Alen oventil fik Vandet Overhaand, og Bjergene bleve skjulte.
21 Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
Saa udaandede alt Kød, som rørte sig paa Jorden, af Fugle og af Kvæg og af vilde Dyr og af al den Vrimmel, som vrimlede paa Jorden, og hvert Menneske.
22 Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
Alt det, som havde Livs Aande i sin Næse, alt det, som var paa det tørre, døde.
23 Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
Og hvert Væsen udslettedes, som var paa Jorden, fra Mennesket indtil Kvæg, indtil Kryb og indtil Fugle under Himmelen, og de bleve udslettede af Jorden; og Noa blev alene igen, og hvad der var med ham i Arken.
24 Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.
Og Vandet havde Overhaand over Jorden hundrede og halvtredsindstyve Dage.

< Farawa 7 >

The Great Flood
The Great Flood