< Farawa 6 >

1 Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
Or il arriva que quand les hommes eurent commencé à se multiplier sur la terre, et qu'ils eurent engendré des filles,
2 sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
Les fils de Dieu voyant que les filles des hommes étaient belles, prirent pour leurs femmes de toutes celles qu'ils choisirent.
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
Et l'Eternel dit: Mon Esprit ne plaidera point à toujours avec les hommes, car aussi ils ne sont que chair; mais leurs jours seront six vingts ans.
4 Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
Il y avait en ce temps-là des géants sur la terre, lors, dis-je, que les fils de Dieu se furent joints avec les filles des hommes, et qu'elles leur eurent fait des enfants. Ce sont ces puissants hommes qui de tout temps ont été des gens de renom.
5 Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
Et l'Eternel voyant que la malice des hommes était très-grande sur la terre, et que toute l'imagination des pensées de leur cœur n'était que mal en tout temps;
6 Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
Se repentit d'avoir fait l'homme sur la terre, et en eut du déplaisir dans son cœur.
7 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
Et l'Eternel dit: J'exterminerai de dessus la terre les hommes que j'ai créés, depuis les hommes jusqu'au bétail, jusqu'aux reptiles, et même jusqu'aux oiseaux des cieux; car je me repens de les avoir faits.
8 Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
Mais Noé trouva grâce devant l'Eternel.
9 Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
Ce sont ici les générations de Noé. Noé fut un homme juste [et] intègre en son temps, marchant avec Dieu.
10 Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
Et Noé engendra trois fils, Sem, Cam, et Japheth.
11 Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
Et la terre était corrompue devant Dieu, et remplie d'extorsion.
12 Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
Dieu donc regarda la terre, et voici elle était corrompue; car toute chair avait corrompu sa voie sur la terre.
13 Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
Et Dieu dit à Noé: La fin de toute chair est venue devant moi; car ils ont rempli la terre d'extorsion, et voici, je les détruirai avec la terre.
14 Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
Fais-toi une arche de bois de gopher; tu feras l'arche par loges, et la calfeutreras de bitume par dedans et par dehors.
15 Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
Et tu la feras en cette manière; la longueur de l'arche sera de trois cents coudées; sa largeur de cinquante coudées, et sa hauteur de trente coudées.
16 Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
Tu donneras du jour à l'arche, et feras son comble d'une coudée [de hauteur], et tu mettras la porte de l'arche à son coté, et tu la feras avec un bas, un second, et un troisième étage.
17 Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
Et voici, je ferai venir un déluge d'eau sur la terre, pour détruire toute chair en laquelle il y a esprit de vie sous les cieux; et tout ce qui est sur la terre expirera.
18 Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
Mais j'établirai mon alliance avec toi; et tu entreras dans l'arche toi et tes fils, et ta femme, et les femmes de tes fils avec toi.
19 Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
Et de tout ce qui a vie d'entre toute chair tu en feras entrer deux [de chaque espèce] dans l'arche, pour les conserver en vie avec toi, savoir le mâle et la femelle;
20 Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
Des oiseaux, selon leur espèce des bêtes à quatre pieds, selon leur espèce, [et] de tous reptiles, selon leur espèce. Il y entrera de tous par paires avec toi, afin que tu les conserves en vie.
21 Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
Prends aussi avec toi de toute chose qu'on mange, et la retire à toi, afin qu'elle serve pour ta nourriture, et pour celle des animaux.
22 Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
Et Noé fit selon tout ce que Dieu lui avait commandé; il le fit ainsi.

< Farawa 6 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water