< Farawa 6 >
1 Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
Lorsque les hommes commencèrent à se multiplier sur la surface de la terre et que des filles leur naquirent,
2 sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
les fils de Dieu virent que les filles des hommes étaient belles, et ils prirent pour femmes toutes celles qu'ils voulurent.
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
Yahvé dit: « Mon Esprit ne luttera pas toujours avec l'homme, car lui aussi est chair; aussi ses jours seront-ils de cent vingt ans. »
4 Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
Les Nephilim étaient sur la terre en ces jours-là, et aussi après, lorsque les fils de Dieu s'approchèrent des filles des hommes et eurent des enfants avec elles. Ce sont les hommes puissants d'autrefois, les hommes de renom.
5 Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
L'Éternel vit que la méchanceté de l'homme était grande sur la terre, et que toutes les imaginations des pensées du cœur de l'homme étaient continuellement mauvaises.
6 Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
L'Éternel se désolait d'avoir créé l'homme sur la terre, et cela lui faisait de la peine dans son cœur.
7 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
Yahvé dit: « Je vais détruire l'homme que j'ai créé sur la surface de la terre, l'homme, les animaux, les reptiles et les oiseaux du ciel, car je suis désolé de les avoir créés. »
8 Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
Mais Noé trouva grâce aux yeux de Yahvé.
9 Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
Voici l'histoire des générations de Noé: Noé était un homme juste, irréprochable parmi les gens de son temps. Noé marchait avec Dieu.
10 Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
Noé est devenu le père de trois fils: Sem, Cham et Japhet.
11 Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
La terre était corrompue devant Dieu, et la terre était remplie de violence.
12 Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
Dieu regarda la terre et vit qu'elle était corrompue, car toute chair avait corrompu sa voie sur la terre.
13 Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
Dieu dit à Noé: « Je vais faire disparaître toute chair, car la terre est remplie de violence par elle. Voici que je vais les détruire, eux et la terre.
14 Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
Fais un navire en bois de gopher. Tu feras des chambres dans le navire, et tu le scelleras de poix à l'intérieur et à l'extérieur.
15 Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
Voici comment tu le feras. La longueur du navire sera de trois cents coudées, sa largeur de cinquante coudées et sa hauteur de trente coudées.
16 Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
Tu feras un toit dans le navire, et tu l'achèveras jusqu'à une coudée en haut. Tu placeras la porte du navire sur son côté. Tu le feras avec un premier, un deuxième et un troisième étage.
17 Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
Moi, je ferai venir le déluge d'eau sur cette terre, pour détruire toute chair ayant souffle de vie sous le ciel. Tout ce qui est sur la terre mourra.
18 Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
Mais j'établirai mon alliance avec vous. Vous monterez dans le navire, toi, tes fils, ta femme et les femmes de tes fils avec toi.
19 Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
De tous les êtres vivants de toute chair, tu en feras entrer deux dans le navire, pour les garder en vie avec toi. Ils seront mâle et femelle.
20 Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
Des oiseaux selon leur espèce, du bétail selon son espèce, de tout reptile du sol selon son espèce, deux de chaque espèce viendront à toi, pour les garder en vie.
21 Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
Prends avec toi une partie de tout ce qui se mange, et ramasse-le pour toi; cela te servira de nourriture, à toi et à eux. »
22 Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
Noé fit ainsi. Il fit tout ce que Dieu lui avait ordonné.