< Farawa 6 >
1 Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
And it came to pass, when men began to multiply on the face of the earth, and daughters were born to them,
2 sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
That the sons of God saw the daughters of men that they were fair; and they took them wives of all which they chose.
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
And the LORD said, My spirit shall not always strive with man, for that he also is flesh: yet his days shall be an hundred and twenty years.
4 Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
There were giants in the earth in those days; and also after that, when the sons of God came in to the daughters of men, and they bore children to them, the same became mighty men which were of old, men of renown.
5 Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
And God saw that the wickedness of man was great in the earth, and that every imagination of the thoughts of his heart was only evil continually.
6 Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
And it repented the LORD that he had made man on the earth, and it grieved him at his heart.
7 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
And the LORD said, I will destroy man whom I have created from the face of the earth; both man, and beast, and the creeping thing, and the fowls of the air; for it repents me that I have made them.
8 Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
But Noah found grace in the eyes of the LORD.
9 Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
These are the generations of Noah: Noah was a just man and perfect in his generations, and Noah walked with God.
10 Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
And Noah begat three sons, Shem, Ham, and Japheth.
11 Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
The earth also was corrupt before God, and the earth was filled with violence.
12 Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
And God looked on the earth, and, behold, it was corrupt; for all flesh had corrupted his way on the earth.
13 Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
And God said to Noah, The end of all flesh is come before me; for the earth is filled with violence through them; and, behold, I will destroy them with the earth.
14 Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
Make you an ark of gopher wood; rooms shall you make in the ark, and shall pitch it within and without with pitch.
15 Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
And this is the fashion which you shall make it of: The length of the ark shall be three hundred cubits, the breadth of it fifty cubits, and the height of it thirty cubits.
16 Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
A window shall you make to the ark, and in a cubit shall you finish it above; and the door of the ark shall you set in the side thereof; with lower, second, and third stories shall you make it.
17 Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
And, behold, I, even I, do bring a flood of waters on the earth, to destroy all flesh, wherein is the breath of life, from under heaven; and every thing that is in the earth shall die.
18 Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
But with you will I establish my covenant; and you shall come into the ark, you, and your sons, and your wife, and your sons’ wives with you.
19 Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
And of every living thing of all flesh, two of every sort shall you bring into the ark, to keep them alive with you; they shall be male and female.
20 Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
Of fowls after their kind, and of cattle after their kind, of every creeping thing of the earth after his kind, two of every sort shall come to you, to keep them alive.
21 Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
And take you to you of all food that is eaten, and you shall gather it to you; and it shall be for food for you, and for them.
22 Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
Thus did Noah; according to all that God commanded him, so did he.