< Farawa 6 >

1 Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
People started to increase in number and spread out across the earth. Daughters were born to them,
2 sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
and the sons of God saw that these women were beautiful, and they took whichever ones they wanted.
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
Then the Lord said, “My life-giving Spirit will not remain in these people forever, because they are only mortal. The time they have left will be 120 years.”
4 Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
There were giants on earth in those days, and also later on. They were born after the sons of God slept with the daughters of these people. Their sons became the great warriors and famous men of ancient times.
5 Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
The Lord saw how terribly evil people on earth had become—every single thought in their minds was evil all the time!
6 Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
The Lord was sorry he'd made human beings to live on the earth; it made him very sad to think about it.
7 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
So the Lord said, “I'm going to wipe out these people I created from the earth, and not only them but also the animals, the creatures that run along the ground, and the birds, because I'm sorry I made them.”
8 Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
But the Lord was pleased with Noah.
9 Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
This is the story of Noah and his family. Noah was a man of integrity, living a moral life among the people of his time. He had a close relationship with God.
10 Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
Noah had three sons: Shem, Ham, and Japheth.
11 Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
God saw how corrupt the whole world had become, full of violent and lawless people.
12 Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
God recognized that the corruption in the world was due to everyone on earth living corrupt lives.
13 Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
So God told Noah, “I have decided to put an end to all people on earth because they are all violent and lawless. I myself am going to destroy all of them, along with the earth.
14 Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
Build an ark out of cypress wood. Make rooms inside the ark, and coat it with tar, both inside and out.
15 Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
This is how to build it: the ark is to measure 300 cubits long, 50 cubits wide, and 30 cubits high.
16 Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
Make a roof for the ark, leaving a cubit-wide opening between the roof and the top of the sides. Put a door in the side of the ark, and construct three decks inside.
17 Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
I myself am going to flood the earth with water that will destroy everything that breathes, Every living thing everywhere on earth will die.
18 Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
But I will keep my agreement with you. You are to go into the ark, taking with you your wife and your sons and their wives.
19 Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
Take a pair, male and female, of every kind of animal into the ark and make sure you keep them alive.
20 Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
The same applies to every kind of bird, livestock, and the creatures that run along the ground—a pair of every kind will come to you so they can be kept alive.
21 Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
Take all kinds of food with you too. Store it so you and the animals will have enough to eat.”
22 Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
Noah did exactly what God ordered him to do.

< Farawa 6 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water