< Farawa 50 >

1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
Yusuf kendini babasının üzerine attı, ağlayarak onu öptü.
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
Babasının cesedini mumyalamaları için özel hekimlerine buyruk verdi. Hekimler İsrail'i mumyaladılar.
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
Bu iş kırk gün sürdü. Mumyalama için bu süre gerekliydi. Mısırlılar İsrail için yetmiş gün yas tuttu.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
Yas günleri geçince, Yusuf firavunun ev halkına, “Eğer benden hoşnut kaldınızsa, lütfen firavunla konuşun” dedi,
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
“Babam bana ant içirdi: ‘Ölmek üzereyim. Beni Kenan ülkesinde kendim için kazdırdığım mezara gömeceksin’ dedi. Şimdi lütfen firavuna bildirin, izin versin gideyim, babamı gömüp geleyim.”
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
Firavun, “Git, babanı göm, andını yerine getir” dedi.
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
Böylece Yusuf babasını gömmeye gitti. Firavunun bütün görevlileri, sarayın ve Mısır'ın ileri gelenleri ona eşlik etti.
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
Yusuf'un bütün ailesi, kardeşleri, babasının ev halkı da onunla birlikteydi. Yalnız çocukları, davarlarla sığırları Goşen'de bıraktılar.
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
Arabalarla atlılar da onları izledi. Büyük bir alay oluşturdular.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
Şeria Irmağı'nın doğusunda Atat Harmanı'na varınca, yüksek sesle, acı acı ağıt yaktılar. Yusuf babası için yedi gün yas tuttu.
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
O bölgede yaşayan Kenanlılar, Atat Harmanı'ndaki yası görünce, “Mısırlılar ne kadar hüzünlü yas tutuyor!” dediler. Bu yüzden, Şeria Irmağı'nın doğusundaki bu yere Avel-Misrayim adı verildi.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
Yakup'un oğulları, babalarının vermiş olduğu buyruğu tam tamına yerine getirdiler.
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
Onu Kenan ülkesine götürüp Mamre yakınlarında Makpela Tarlası'ndaki mağaraya gömdüler. O mağarayı mezar yapmak üzere tarlayla birlikte Hititli Efron'dan İbrahim satın almıştı.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
Yusuf babasını gömdükten sonra, kendisi, kardeşleri ve onunla birlikte babasını gömmeye gelenlerin hepsi Mısır'a döndüler.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
Babalarının ölümünden sonra Yusuf'un kardeşleri, “Belki Yusuf bize kin besliyordur” dediler, “Ya ona yaptığımız kötülüğe karşılık bizden öç almaya kalkarsa?”
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
Böylece Yusuf'a haber gönderdiler: “Babamız ölmeden önce Yusuf'a şöyle deyin diye buyurmuştu: ‘Kardeşlerin sana kötülük yaptılar, lütfen onların suçunu, günahını bağışla.’ Ne olur şimdi günahımızı bağışla. Biz babanın Tanrısı'nın kullarıyız.” Yusuf bu haberi alınca ağladı.
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
Bunun üzerine kardeşleri gidip onun önünde yere kapanarak, “Senin köleniz” dediler.
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
Yusuf, “Korkmayın” dedi, “Ben Tanrı mıyım?
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
Siz bana kötülük düşündünüz, ama Tanrı bugün olduğu gibi birçok halkın yaşamını korumak için o kötülüğü iyiliğe çevirdi.
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
Korkmanıza gerek yok, size de çocuklarınıza da bakacağım.” Yüreklerine dokunacak güzel sözlerle onlara güven verdi.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
Yusuf'la babasının ev halkı Mısır'a yerleştiler. Yusuf yüz on yıl yaşadı.
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
Efrayim'in üç göbek çocuklarını gördü. Manaşşe'nin oğlu Makir'in çocukları onun elinde doğdu.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
Yusuf yakınlarına, “Ben ölmek üzereyim” dedi, “Ama Tanrı kesinlikle size yardım edecek; sizi İbrahim'e, İshak'a, Yakup'a ant içerek söz verdiği topraklara götürecek.”
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
Sonra onlara ant içirerek, “Tanrı kesinlikle size yardım edecek” dedi, “O zaman kemiklerimi buradan götürürsünüz.”
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
Yusuf yüz on yaşında öldü. Onu mumyalayıp Mısır'da bir tabuta koydular.

< Farawa 50 >