< Farawa 50 >

1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
Då föll Josef ned över sin faders ansikte och grät över honom och kysste honom.
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
Och Josef bjöd läkarna som han hade i sin tjänst att de skulle balsamera hans fader; och läkarna balsamerade Israel.
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
Därtill åtgingo fyrtio dagar; så många dagar åtgå nämligen för balsamering. Och egyptierna begräto honom i sjuttio dagar.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
Men när gråtodagarna efter honom voro förbi, talade Josef till Faraos husfolk och sade: "Om jag har funnit nåd för edra ögon, så framfören till Farao dessa mina ord:
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
Min fader har tagit en ed av mig och sagt: 'När jag är död, begrav mig då i den grav som jag har låtit gräva åt mig i Kanaans land.' Så låt mig nu fara ditupp och begrava min fader; sedan skall jag komma tillbaka igen."
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
Farao svarade: "Far ditupp och begrav din fader, efter den ed som han har tagit av dig."
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
Då for Josef upp för att begrava sin fader, och med honom foro alla Faraos tjänare, de äldste i hans hus och alla de äldste i Egyptens land,
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
därtill allt Josefs husfolk och hans bröder och hans faders husfolk; allenast sina kvinnor och barn, och sina får och fäkreatur lämnade de kvar i landet Gosen.
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
Och med honom foro ditupp både vagnar och ryttare; och det var en mycket stor skara.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
När de nu kommo till Goren-Haatad, på andra sidan Jordan, höllo de där en mycket stor och högtidlig dödsklagan, och han anställde en sorgefest efter sin fader i sju dagar.
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
Och när landets inbyggare, kananéerna, sågo sorgefesten i Goren-Haatad, sade de: "Det är en högtidlig sorgefest som egyptierna här hålla." Därav fick stället namnet Abel-Misraim; det ligger på andra sidan Jordan.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
Och hans söner gjorde med honom såsom han hade bjudit dem:
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
hans söner förde honom till Kanaans land och begrovo honom i grottan på åkern i Makpela, den åker som Abraham hade köpt till egen grav av hetiten Efron, gent emot Mamre.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
Och sedan Josef hade begravit sin fader, vände han tillbaka till Egypten med sina bröder och alla dem som hade farit upp med honom för att begrava hans fader.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
Men när Josefs bröder sågo att deras fader var död, tänkte de: "Kanhända skall Josef nu bliva hätsk mot oss och vedergälla oss allt det onda som vi hava gjort mot honom."
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
Därför sände de bud till Josef och läto säga: "Din fader bjöd oss så före sin död:
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
'Så skolen I säga till Josef: Käre, förlåt dina bröder vad de hava brutit och syndat, i det att de hava handlat så illa mot dig.' Förlåt alltså nu din faders Guds tjänare vad de hava brutit." Och Josef grät, när de läto säga detta till honom.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
Sedan kommo ock hans bröder själva och föllo ned för honom och sade: "Se, vi vilja vara tjänare åt dig."
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
Men Josef sade till dem: "Frukten icke. Hållen I då mig för Gud?
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
I tänkten ont mot mig, men Gud har tänkt det till godo, för att låta det ske, som nu har skett, och så behålla mycket folk vid liv.
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
Frukten därför nu icke; jag skall försörja eder och edra kvinnor och barn." Och han tröstade dem och talade vänligt med dem.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
Och Josef bodde kvar i Egypten med sin faders hus; och Josef blev ett hundra tio år gammal.
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
Och Josef fick se Efraims barn till tredje led; också av Makir, Manasses son, föddes barn i Josefs sköte.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
Och Josef sade till sina bröder: "Jag dör, men Gud skall förvisso se till eder, och föra eder upp från detta land till det land som han med ed har lovat åt Abraham, Isak och Jakob."
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
Och Josef tog en ed av Israels barn och sade: "När nu Gud ser till eder, fören då mina ben härifrån."
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
Och Josef dog, när han var ett hundra tio år gammal. Och man balsamerade honom, och han lades i en kista, i Egypten.

< Farawa 50 >