< Farawa 50 >

1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
Wtedy Józef przypadł do twarzy swego ojca i płakał nad nim, i całował go.
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
Potem Józef rozkazał swoim sługom, lekarzom, aby zabalsamowali jego ojca. I lekarze zabalsamowali Izraela.
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
I minęło czterdzieści dni, bo tyle trwa balsamowanie. Egipcjanie opłakiwali go przez siedemdziesiąt dni.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
Po upływie dni żałoby Józef powiedział do domowników faraona: Jeśli znalazłem teraz łaskę w waszych oczach, powiedzcie, proszę, do uszu faraona:
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
Mój ojciec zobowiązał mnie przysięgą i powiedział: Oto ja umieram. Pogrzebiesz mnie w moim grobie, który sobie wykopałem w ziemi Kanaan. Teraz, proszę, pozwól mi pojechać i pogrzebać mego ojca, a potem wrócę.
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
Faraon powiedział: Jedź i pogrzeb twego ojca, jak cię zobowiązał przysięgą.
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
Józef pojechał więc, aby pogrzebać swego ojca. Jechali też z nim wszyscy słudzy faraona, także starsi jego domu i wszyscy starsi ziemi Egiptu;
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
I cały dom Józefa, jego bracia i dom jego ojca. Tylko swoje dzieci, swoje owce i swoje woły zostawili w ziemi Goszen.
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
Wyruszyły też z nimi wozy i wyruszyli jeźdźcy. A orszak był bardzo wielki.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
I przyjechali aż do klepiska Atad, które jest za Jordanem, i tam opłakiwali go wielkim i bardzo głębokim lamentem. Józef przez siedem dni obchodził żałobę po swym ojcu.
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
A gdy obywatele ziemi Kanaan zobaczyli tę żałobę na klepisku Atad, mówili: To ciężka żałoba Egipcjan. Dlatego nazwano to miejsce Ebel-Misraim; leży ono za Jordanem.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
Jego synowie uczynili więc z nim tak, jak im rozkazał.
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
Jego synowie zawieźli go do ziemi Kanaan i pogrzebali go w jaskini na polu Makpela naprzeciwko Mamre, którą kupił Abraham wraz z polem od Efrona Chetyty jako grób na własność.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
Po pogrzebie swego ojca Józef wrócił do Egiptu wraz ze swymi braćmi i ze wszystkimi, którzy pojechali z nim na pogrzeb jego ojca.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
A bracia Józefa, widząc, że ich ojciec umarł, mówili: Może Józef będzie nas nienawidził i odpłaci nam sowicie za to wszystko zło, które mu uczyniliśmy.
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
Kazali więc powiedzieć do Józefa: Twój ojciec, zanim umarł, nakazał:
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
Tak powiedzcie Józefowi: Proszę, wybacz teraz przestępstwo twoich braci i ich grzech, że wyrządzili ci zło. Proszę, wybacz teraz występek sługom Boga twego ojca. I Józef płakał, gdy to mówili do niego.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
I jego bracia podeszli, i upadli przed nim, mówiąc: Oto jesteśmy twoimi sługami.
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
Józef powiedział do nich: Nie bójcie się. Czyż ja jestem na miejscu Boga?
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
Obmyśliliście zło przeciwko mnie, ale Bóg obrócił to w dobro, żeby sprawić to, co się dziś dzieje, aby zachować tak wielki lud.
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
Teraz więc nie bójcie się. Ja będę żywić was i wasze dzieci. I tak ich pocieszał, i serdecznie z nimi rozmawiał.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
I Józef mieszkał w Egipcie, on sam i dom jego ojca. A Józef żył sto dziesięć lat.
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
Józef oglądał synów Efraima aż do trzeciego pokolenia. Także synowie Makira, syna Manassesa, wychowali się na kolanach Józefa.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
Potem Józef powiedział do swoich braci: Ja umrę, ale Bóg na pewno was nawiedzi i wyprowadzi z tej ziemi do ziemi, którą przysiągł Abrahamowi, Izaakowi i Jakubowi.
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
Józef zobowiązał więc przysięgą synów Izraela i powiedział: Bóg na pewno was nawiedzi, a wtedy zabierzcie stąd moje kości.
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
I Józef umarł, mając sto dziesięć lat. Zabalsamowano go i złożono do trumny w Egipcie.

< Farawa 50 >