< Farawa 50 >
1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
Joseph se jeta sur le visage de son père, pleura sur lui et le baisa.
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
Puis il ordonna aux médecins à son service d’embaumer son père, et les médecins embaumèrent Israël.
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
Ils y employèrent quarante jours, car c’est le temps que l’on emploie à embaumer; et les Egyptiens le pleurèrent soixante-dix jours.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
Quand les jours de son deuil furent passés, Joseph s’adressa aux gens de la maison de Pharaon, et leur dit: « Si j’ai trouvé grâce à vos yeux, rapportez ceci, je vous prie, aux oreilles de Pharaon:
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
Mon père m’a fait jurer, en disant: Voici que je vais mourir; tu m’enterreras dans le sépulcre que je me suis creusé au pays de Canaan. Je voudrais donc y monter pour enterrer mon père; et je reviendrai. »
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
Pharaon répondit: « Monte et enterre ton père, comme il te l’a fait jurer. »
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
Joseph monta pour enterrer son père. Avec lui montèrent tous les serviteurs de Pharaon, les anciens de sa maison, et tous les anciens du pays d’Égypte,
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
toute la maison de Joseph, ses frères et la maison de son père: ils ne laissèrent dans le pays de Gessen que leurs petits enfants, leurs brebis et leurs bœufs.
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
Il montait encore avec Joseph des chars et des cavaliers, en sorte que le cortège était très nombreux.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
Arrivés à l’aire d’Atad, qui est au delà du Jourdain, ils firent entendre de grandes et profondes lamentations, et Joseph célébra en l’honneur de son père un deuil de sept jours.
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
Les habitants du pays, les Chananéens, ayant vu ce deuil dans l’aire d’Atad, dirent: « Voilà un grand deuil parmi les Egyptiens! » C’est pourquoi l’on a donné le nom d’Abel-Mitsraïm à ce lieu, qui est au delà du Jourdain.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
Les fils de Jacob firent donc envers lui comme il leur avait commandé.
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
Ses fils le transportèrent au pays de Canaan et l’enterrèrent dans la caverne du champ de Macpéla, qu’Abraham avait acquise d’Ephron le Hittite, avec le champ, pour avoir un sépulcre qui lui appartint, vis-à-vis de Mambré.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
Après avoir enterré son père, Joseph retourna en Égypte avec ses frères et tous ceux qui étaient montés avec lui pour enterrer son père.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
Quand les frères de Joseph virent que leur père était mort, ils dirent: « Si Joseph nous prenait en haine, et nous rendait tout le mal que nous lui avons fait! »
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
Et ils firent dire à Joseph: « Ton père a donné cet ordre avant de mourir:
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
Vous parlerez ainsi à Joseph: Oh! pardonne le crime de tes frères et leur péché, car ils t’ont fait du mal! Maintenant donc, je te prie, pardonne le crime des serviteurs du Dieu de ton père. » Joseph pleura, en entendant ces paroles.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
Ses frères vinrent eux-mêmes se prosterner devant lui, en disant: « Nous sommes tes serviteurs. »
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
Joseph leur dit: « Soyez sans crainte; car suis-je à la place de Dieu?
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
Vous aviez dans la pensée de me faire du mal; mais Dieu avait dans la sienne d’en faire sortir du bien, afin d’accomplir ce qui arrive aujourd’hui, afin de conserver la vie à un peuple nombreux.
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
Soyez donc sans crainte; je vous entretiendrai, vous et vos enfants. » C’est ainsi qu’il les consola, en parlant à leurs cœurs.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
Joseph demeura en Égypte, lui et la maison de son père. Il vécut cent dix ans.
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
Joseph vit les fils d’Ephraïm jusqu’à la troisième génération; des fils de Machir, fils de Manassé, naquirent aussi sur les genoux de Joseph.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
Joseph dit à ses frères: « Pour moi, je vais mourir; mais Dieu vous visitera certainement et vous fera remonter de ce pays dans le pays qu’il a juré de donner à Abraham, à Isaac et à Jacob. »
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
Joseph fit jurer les fils d’Israël, en disant: « Certainement Dieu vous visitera, et vous ferez remonter mes os d’ici. »
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
Joseph mourut, âgé de cent dix ans. On l’embauma et on le mit dans un cercueil en Égypte.