< Farawa 50 >

1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
And Joseph falls on his father’s face, and weeps over him, and kisses him;
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
and Joseph commands his servants, the physicians, to embalm his father, and the physicians embalm Israel;
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
and they fulfill for him forty days, for so they fulfill the days of the embalmed, and the Egyptians weep for him seventy days.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
And the days of his weeping pass away, and Joseph speaks to the house of Pharaoh, saying, “Now if I have found grace in your eyes, please speak in the ears of Pharaoh, saying,
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
My father caused me to swear, saying, Behold, I am dying; in my burying-place which I have prepared for myself in the land of Canaan, there you bury me; and now, please let me go up and bury my father, then I return”;
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
and Pharaoh says, “Go up and bury your father, as he caused you to swear.”
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
And Joseph goes up to bury his father, and all [the] servants of Pharaoh go up with him, [the] elderly of his house, and all [the] elderly of the land of Egypt,
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
and all the house of Joseph, and his brothers, and the house of his father; only their infants, and their flock, and their herd, have they left in the land of Goshen;
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
and there go up with him both chariot and horsemen, and the camp is very great.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
And they come to the threshing-floor of Atad, which [is] beyond the Jordan, and they lament there, a lamentation great and very grievous; and he makes for his father a mourning seven days,
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
and the inhabitant of the land, the Canaanite, sees the mourning in the threshing-floor of Atad and says, “A grievous mourning [is] this to the Egyptians”; therefore [one] has called its name “The mourning of the Egyptians,” which [is] beyond the Jordan.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
And his sons do to him so as he commanded them,
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
and his sons carry him away to the land of Canaan, and bury him in the cave of the field of Machpelah, which Abraham bought with the field for a possession of a burying-place, from Ephron the Hittite, on the front of Mamre.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
And Joseph turns back to Egypt, he and his brothers, and all who are going up with him to bury his father, after his burying his father.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
And the brothers of Joseph see that their father is dead, and say, “Perhaps Joseph hates us, and certainly returns to us all the evil which we did with him.”
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
And they give a charge for Joseph, saying, “Your father commanded before his death, saying,
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
Thus you say to Joseph: Ah, now, please bear with the transgression of your brothers and their sin, for they have done you evil; and now, please bear with the transgression of the servants of the God of your father”; and Joseph weeps in their speaking to him.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
And his brothers also go and fall before him, and say, “Behold, we [are] to you for servants.”
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
And Joseph says to them, “Do not fear, for [am] I in the place of God?
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
As for you, you devised evil against me, [but] God devised it for good, in order to do as [at] this day, to keep alive a numerous people;
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
and now, do not fear: I nourish you and your infants”; and he comforts them, and speaks to their heart.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
And Joseph dwells in Egypt, he and the house of his father, and Joseph lives one hundred and ten years,
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
and Joseph looks on Ephraim’s sons of a third [generation]; sons also of Machir, son of Manasseh, have been born on the knees of Joseph.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
And Joseph says to his brothers, “I am dying, and God certainly inspects you, and has caused you to go up from this land, to the land which He has sworn to Abraham, to Isaac, and to Jacob.”
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
And Joseph causes the sons of Israel to swear, saying, “God certainly inspects you, and you have brought up my bones from this [place].”
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
And Joseph dies, a son of one hundred and ten years, and they embalm him, and he is put into a coffin in Egypt.

< Farawa 50 >