< Farawa 50 >

1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
Тогава Иосиф падна на лицето на баща си, плака върху него и го целува.
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
И Иосиф заповяда на служащите нему лекари да балсамират баща му; и лекарите балсамираха Израиля,
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
като работиха над него напълно четиридесет дена; защото толкова е пълното време за балсамиране; и египтяните го оплакваха седемдесет дена.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
И като преминаха дните на жалейката за него, Иосиф говори на Фараоновия дом, казвайки: Ако съм придобил вашето благоволение, говорете, моля ви се, в ушите на Фараона и речете:
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
Баща ми ме закле, като каза: Виж, аз умирам; в гроба, който се приготвих в Ханаанската земя, там да ме погребеш. Сега, прочее нека отида, моля, да погреба баща; си и ще се върна.
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
А рече Фараон: Иди, погреби баща си, според както те е заклел.
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
И така, Иосиф отиде да погребе баща си; и с него отидоха всичките служители на Фараона, старейшините на дома му, и всичките старейшини на Египетската земя,
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
също и целият дом на Иосифа, братята му, и бащиният му дом; само челядите си, стадата си и добитъка си оставиха в Гесенската земя.
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
Отидоха с него и колесници и конници, тъй че стана много голямо шествие.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
И когато пристигнаха до Атадовото гумно, което е оттатък Иордан, там ридаха твърде много и силно; и Иосиф направи за баща си седемдневна жалейка.
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
А ханаанците, тамошните жители, като видяха жалейката при Атадовото гумно, рекоха: египтяните имат голяма жалейка; затова мястото, което е оттатък Иордан, се наименува Авел-мисраим.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
Тогава синовете на Израиля му сториха, според както им беше заповядал;
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
защото синовете му го пренесоха в Ханаанската земя и го погребаха в пещерата на нивата Махпелах, срещу Мамврий, която пещера Авраам купи заедно с нивата за собствено гробище от хетееца Ефрон.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
И Иосиф, като погреба баща си, върна се в Египет, той и братята му и всички, които бяха отишли с него да погребат баща му.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
А като видяха Иосифовите братя, че умря баща им, думаха си: Може Иосиф да ни намрази и да ни възвърне жестоко всичкото зло, що сме му сторили.
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
Затова пратиха на Иосифа да му кажат: Преди да умре баща ти ни заповяда с думите:
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
Така да кажете на Иосифа: Прости, моля ти се, престъплението на братята си и греха им за злото, което ти сториха. И тъй, прости молим ти се, престъплението на слугите на бащиния ти Бог. А Иосиф се разплака, когато му говориха.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
После отидоха и братята му та паднаха пред него и рекоха: Ето, ние сме ти слуги.
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
А Иосиф им каза: Не бойте се; нима съм аз вместо Бога?
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
Вие наистина намислихте зло против мене; но Бог го намисли за добро, за да действува така, щото да спаси живото на много люде, както и стана днес.
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
Прочее, не бойте се; аз ще храня вас и челядите ви. И утеши ги и говори им любезно.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
Така Иосиф остана да живее в Египет, той и бащиният му дом. И Иосиф живя сто и десет години;
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
и Иосиф видя Ефремови чада от третия род; също и децата на Манасиевия син Махира се родиха на Иосифовите колене.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
След това, Иосиф рече на братята си: Аз умирам; а Бог непременно ще ви посети, и ще ви заведе от тая земя в земята, за която се е клел на Авраама, Исака и Якова.
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
И Иосиф закле потомците на Израиля, като рече: Понеже Бог непременно ще ви посети, то вие да изнесете костите ми от тука.
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
И тъй, Иосиф умря, на възраст сто и десет години; и балсамираха го и положиха го в ковчег в Египет.

< Farawa 50 >