< Farawa 5 >
1 Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
hic est liber generationis Adam in die qua creavit Deus hominem ad similitudinem Dei fecit illum
2 Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
masculum et feminam creavit eos et benedixit illis et vocavit nomen eorum Adam in die qua creati sunt
3 Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
vixit autem Adam centum triginta annis et genuit ad similitudinem et imaginem suam vocavitque nomen eius Seth
4 Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
et facti sunt dies Adam postquam genuit Seth octingenti anni genuitque filios et filias
5 Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
et factum est omne tempus quod vixit Adam anni nongenti triginta et mortuus est
6 Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
vixit quoque Seth centum quinque annos et genuit Enos
7 Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
vixitque Seth postquam genuit Enos octingentis septem annis genuitque filios et filias
8 Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
et facti sunt omnes dies Seth nongentorum duodecim annorum et mortuus est
9 Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
vixit vero Enos nonaginta annis et genuit Cainan
10 Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
post cuius ortum vixit octingentis quindecim annis et genuit filios et filias
11 Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
factique sunt omnes dies Enos nongentorum quinque annorum et mortuus est
12 Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
vixit quoque Cainan septuaginta annis et genuit Malalehel
13 Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
et vixit Cainan postquam genuit Malalehel octingentos quadraginta annos genuitque filios et filias
14 Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
et facti sunt omnes dies Cainan nongenti decem anni et mortuus est
15 Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
vixit autem Malalehel sexaginta quinque annos et genuit Iared
16 Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
et vixit Malalehel postquam genuit Iared octingentis triginta annis et genuit filios et filias
17 Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
et facti sunt omnes dies Malalehel octingenti nonaginta quinque anni et mortuus est
18 Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
vixitque Iared centum sexaginta duobus annis et genuit Enoch
19 Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
et vixit Iared postquam genuit Enoch octingentos annos et genuit filios et filias
20 Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
et facti sunt omnes dies Iared nongenti sexaginta duo anni et mortuus est
21 Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
porro Enoch vixit sexaginta quinque annis et genuit Mathusalam
22 Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
et ambulavit Enoch cum Deo postquam genuit Mathusalam trecentis annis et genuit filios et filias
23 Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
et facti sunt omnes dies Enoch trecenti sexaginta quinque anni
24 Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
ambulavitque cum Deo et non apparuit quia tulit eum Deus
25 Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
vixit quoque Mathusalam centum octoginta septem annos et genuit Lamech
26 Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
et vixit Mathusalam postquam genuit Lamech septingentos octoginta duos annos et genuit filios et filias
27 Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
et facti sunt omnes dies Mathusalae nongenti sexaginta novem anni et mortuus est
28 Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
vixit autem Lamech centum octoginta duobus annis et genuit filium
29 Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
vocavitque nomen eius Noe dicens iste consolabitur nos ab operibus et laboribus manuum nostrarum in terra cui maledixit Dominus
30 Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
vixitque Lamech postquam genuit Noe quingentos nonaginta quinque annos et genuit filios et filias
31 Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
et facti sunt omnes dies Lamech septingenti septuaginta septem anni et mortuus est
32 Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.
Noe vero cum quingentorum esset annorum genuit Sem et Ham et Iafeth