< Farawa 5 >

1 Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
This, is the record of the generations of Adam. In the day when God created man, In the likeness of God, made he him:
2 Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
Male and female, created he them, —and blessed them, and called their name Adam, in the day they were created.
3 Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
And Adam lived a hundred and thirty years, and begat [a son] in his likeness after his image, —and called his name Seth:
4 Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and the days of Adam, after he begat Seth, were eight hundred years, and he begat sons and daughters.
5 Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
So all the days of Adam which he lived, were nine hundred and thirty years, —and he died.
6 Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
And Seth lived a hundred and five years, —and begat Enosh:
7 Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Seth lived, after he begat Enosh, eight hundred and seven years, —and begat sons and daughters:
8 Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Seth were, nine hundred and I twelve years, —and he died.
9 Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
And Enosh lived ninety years, —and begat Kenan;
10 Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Enosh lived after he begat Kenan, eight hundred and fifteen years, —and begat sons and daughters;
11 Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Enosh were nine hundred and five years, —and he died.
12 Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
And Kenan, lived seventy years, —and begat Mahalalel;
13 Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
and Kenan lived after he begat Mahalalel, eight hundred and forty years, —and begat sons and daughters;
14 Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Kenan were, nine hundred and ten years, —and he died.
15 Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
And Mahalalel lived sixty-five years, —and begat Jared;
16 Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
and Mahalalel lived after he begat Jared, eight hundred and thirty years, —and begat sons and daughters;
17 Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Mahalalel were, eight hundred and ninety-five years, —and he died.
18 Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
And Jared lived, a hundred and sixty-two years, and begat Enoch;
19 Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Jared lived after he begat Enoch, eight hundred years, —and begat sons and daughters;
20 Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Jared were, nine hundred and sixty-two years, —and he died.
21 Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
And Enoch lived sixty-five years, —and begat Methuselah;
22 Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Enoch walked with God, after he begat Methuselah, three hundred years, —and begat sons and daughters;
23 Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
and all the days of Enoch were, three hundred and sixty-five years;
24 Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
and Enoch walked with God, —and was not for God had taken him.
25 Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
And Methuselah lived, a hundred and eighty-seven years, —and begat Lamech;
26 Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Methuselah lived, after he begat Lamech, seven hundred and eighty-two years, —and begat sons and daughters;
27 Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Methuselah were, nine hundred and sixty-nine years, —and he died.
28 Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
And Lamech lived, a hundred and eighty-two years, —and begat a son;
29 Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
and he called his name Noah saying, —This, one shall give us rest from our work, And from the grievous toil of our hands, By reason of the ground which Yahweh hath cursed,
30 Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
And Lamech lived, after he begat Noah, five hundred and ninety-five years, —and begat sons and daughters;
31 Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
and all the days of Lamech were seven hundred and seventy-seven years, —and he died.
32 Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.
And Noah was five hundred years old, —and Noah begat Shem, Ham and Japheth.

< Farawa 5 >