< Farawa 5 >
1 Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
This is the booke of the generations of Adam. In the day that God created Adam, in the likenes of God made he him,
2 Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
Male and female created he them, and blessed them, and called their name Adam in the day that they were created.
3 Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
Nowe Adam liued an hundred and thirtie yeeres, and begate a childe in his owne likenes after his image, and called his name Sheth.
4 Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And the dayes of Adam, after he had begotten Sheth, were eight hundreth yeeres, and he begate sonnes and daughters.
5 Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes that Adam liued, were nine hundreth and thirtie yeeres: and he died.
6 Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
And Sheth liued an hundreth and fiue yeeres, and begate Enosh.
7 Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Sheth liued, after he begate Enosh, eight hundreth and seuen yeeres, and begate sonnes and daughters.
8 Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes of Sheth were nine hundreth and twelue yeeres: and he died.
9 Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
Also Enosh liued ninetie yeeres, and begate Kenan.
10 Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Enosh liued, after he begate Kenan, eight hundreth and fifteene yeeres, and begate sonnes and daughters.
11 Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes of Enosh were nine hundreth and fiue yeeres: and he died
12 Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
Likewise Kenan liued seuentie yeeres, and begate Mahalaleel.
13 Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
And Kenan liued, after he begate Mahalaleel, eight hundreth and fourtie yeeres, and begate sonnes and daughters.
14 Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes of Kenan were nine hundreth and tenne yeeres: and he died.
15 Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
Mahalaleel also liued sixtie and fiue yeres, and begate Iered.
16 Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
Also Mahalaleel liued, after he begate Iered, eight hundreth and thirtie yeeres, and begate sonnes and daughters.
17 Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes of Mahalaleel were eight hundreth ninetie and fiue yeeres: and he died.
18 Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
And Iered liued an hundreth sixtie and two yeeres, and begate Henoch.
19 Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Then Iered liued, after he begate Henoch, eight hundreth yeeres, and begate sonnes and daughters.
20 Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes of Iered were nine hundreth sixtie and two yeeres: and he died.
21 Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
Also Henoch liued sixtie and fiue yeeres, and begate Methushelah.
22 Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Henoch walked with God, after he begate Methushelah, three hundreth yeeres, and begate sonnes and daughters.
23 Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
So all the dayes of Henoch were three hundreth sixtie and fiue yeeres.
24 Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
And Henoch walked with God, and he was no more seene: for God tooke him away.
25 Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
Methushelah also liued an hundreth eightie and seuen yeeres, and begate Lamech.
26 Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Methushelah liued, after he begate Lamech, seuen hundreth eightie and two yeeres, and begate sonnes and daughters.
27 Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
So al the dayes of Methushelah were nine hundreth sixtie and nine yeeres: and he died.
28 Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
Then Lamech liued an hundreth eightie and two yeeres, and begate a sonne,
29 Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
And called his name Noah, saying, This same shall comfort vs concerning our worke and sorowe of our hands, as touching the earth, which the Lord hath cursed.
30 Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
And Lamech liued, after he begate Noah, fiue hundreth ninetie and fiue yeeres, and begate sonnes and daughters.
31 Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
So all the dayes of Lamech were seuen hundreth seuentie and seuen yeeres: and he died.
32 Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.
And Noah was fiue hundreth yeere olde. And Noah begate Shem, Ham and Iapheth.