< Farawa 5 >
1 Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
This is the book of the generations of Adam. In the day when God made man, he made him in the image of God;
2 Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
Male and female he made them, naming them Man, and giving them his blessing on the day when they were made.
3 Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
Adam had been living for a hundred and thirty years when he had a son like himself, after his image, and gave him the name of Seth:
4 Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And after the birth of Seth, Adam went on living for eight hundred years, and had sons and daughters:
5 Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Adam's life were nine hundred and thirty: and he came to his end.
6 Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
And Seth was a hundred and five years old when he became the father of Enosh:
7 Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And he went on living after the birth of Enosh for eight hundred and seven years, and had sons and daughters:
8 Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Seth's life were nine hundred and twelve: and he came to his end.
9 Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
And Enosh was ninety years old when he became the father of Kenan:
10 Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And after the birth of Kenan, Enosh went on living for eight hundred and fifteen years, and had sons and daughters:
11 Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Enosh were nine hundred and five: and he came to his end.
12 Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
And Kenan was seventy years old when he became the father of Mahalalel:
13 Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
And after the birth of Mahalalel, Kenan went on living for eight hundred and forty years, and had sons and daughters:
14 Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Kenan's life were nine hundred and ten; and he came to his end.
15 Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
And Mahalalel was sixty-five years old when he became the father of Jared:
16 Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
And after the birth of Jared, Mahalalel went on living for eight hundred and thirty years, and had sons and daughters:
17 Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Mahalalel's life were eight hundred and ninety-five: and he came to his end.
18 Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
And Jared was a hundred and sixty-two years old when he became the father of Enoch:
19 Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Jared went on living after the birth of Enoch for eight hundred years, and had sons and daughters:
20 Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Jared's life were nine hundred and sixty-two: and he came to his end.
21 Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
And Enoch was sixty-five years old when he became the father of Methuselah:
22 Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And after the birth of Methuselah, Enoch went on in God's ways for three hundred years, and had sons and daughters:
23 Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
And all the years of Enoch's life were three hundred and sixty-five:
24 Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
And Enoch went on in God's ways: and he was not seen again, for God took him.
25 Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
And Methuselah was a hundred and eighty-seven years old when he became the father of Lamech:
26 Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And after the birth of Lamech, Methuselah went on living for seven hundred and eighty-two years, and had sons and daughters:
27 Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Methuselah's life were nine hundred and sixty-nine: and he came to his end.
28 Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
And Lamech was a hundred and eighty-two years old when he had a son:
29 Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
And he gave him the name of Noah, saying, Truly, he will give us rest from our trouble and the hard work of our hands, because of the earth which was cursed by God.
30 Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
And after the birth of Noah, Lamech went on living for five hundred and ninety-five years, and had sons and daughters:
31 Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
And all the years of Lamech's life were seven hundred and seventy-seven: and he came to his end.
32 Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.
And when Noah was five hundred years old, he became the father of Shem, Ham, and Japheth.