< Farawa 49 >

1 Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
Poslije sazva Jakov sinove svoje i reèe: skupite se da vam javim šta æe vam biti do pošljetka.
2 “Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
Skupite se i poslušajte, sinovi Jakovljevi, poslušajte Izrailja oca svojega.
3 “Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
Ruvime, ti si prvenac moj, krjepost moja i poèetak sile moje; prvi gospodstvom i prvi snagom.
4 Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
Navro si kao voda; neæeš biti prvi; jer si stao na postelju oca svojega i oskvrnio je legav na nju.
5 “Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
Simeun i Levije, braæa, maèevi su im oružje nepravdi.
6 Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
U tajne njihove da ne ulazi duša moja, sa zborom njihovijem da se ne sastavlja slava moja; jer u gnjevu svojem pobiše ljude, i za svoje veselje pokidaše volove.
7 La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
Proklet da je gnjev njihov, što bješe nagao, i ljutina njihova, što bješe žestoka; razdijeliæu ih po Jakovu, i rasuæu ih po Izrailju.
8 “Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
Juda, tebe æe hvaliti braæa tvoja, a ruka æe ti biti za vratom neprijateljima tvojim, i klanjaæe ti se sinovi oca tvojega.
9 Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
Laviæu Juda! s plijena si se vratio, sine moj; spusti se i leže kao lav i kao ljuti lav; ko æe ga probuditi?
10 Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
Palica vladalaèka neæe se odvojiti od Jude niti od nogu njegovijeh onaj koji postavlja zakon, dokle ne doðe onaj kome pripada, i njemu æe se pokoravati narodi.
11 Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
Veže za èokot magare svoje, i za plemenitu lozu mlade od magarice svoje; u vinu pere haljinu svoju i ogrtaè svoj u soku od grožða.
12 Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
Oèi mu se crvene od vina i zubi bijele od mlijeka.
13 “Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
Zavulon æe živjeti pokraj mora i gdje pristaju laðe, a meða æe mu biti do Sidona.
14 “Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
Isahar je magarac jak u kostima, koji leži u toru,
15 Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
I vidjev da je poèivanje dobro i da je zemlja mila, sagnuæe ramena svoja da nosi, i plaæaæe danak.
16 “Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
Dan æe suditi svojemu narodu, kao jedno izmeðu plemena Izrailjevih.
17 Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
Dan æe biti zmija na putu i guja na stazi, koja ujeda konja za kièicu, te pada konjik nauznako.
18 “Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
Gospode, tebe èekam da me izbaviš.
19 “Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
A Gad, njega æe vojska svladati; ali æe najposlije on nadvladati.
20 “Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
U Asira æe biti obilata hrana, i on æe davati slasti carske.
21 “Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
Neftalim je košuta puštena, i govoriæe lijepe rijeèi.
22 “Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
Josif je rodna grana, rodna grana kraj izvora, kojoj se ogranci raširiše svrh zida.
23 Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
Ako ga i ucvijeliše ljuto i strijeljaše na nj, i biše mu neprijatelji strijelci,
24 Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
Opet osta jak luk njegov i ojaèaše mišice ruku njegovijeh od ruku jakoga Boga Jakovljeva, odakle posta pastir, kamen Izrailju,
25 saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
Od silnoga Boga oca tvojega, koji æe ti pomagati, i od svemoguæega, koji æe te blagosloviti blagoslovima ozgo s neba, blagoslovima ozdo iz bezdana, blagoslovima od dojaka i od materice.
26 Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
Blagoslovi oca tvojega nadvisiše blagoslove mojih starijeh svrh brda vjeènijeh, neka budu nad glavom Josifovom i nad tjemenom odvojenoga izmeðu braæe.
27 “Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
Venijamin je vuk grabljivi, jutrom jede lov, a veèerom dijeli plijen.
28 Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
Ovo su dvanaest plemena Izrailjevih, i ovo im otac izgovori kad ih blagoslovi, svako blagoslovom njegovijem blagoslovi ih.
29 Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
Potom im zapovjedi i reèe im: kad se priberem k rodu svojemu, pogrebite me kod otaca mojih u peæini koja je na njivi Efrona Hetejina,
30 kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
U peæini koja je na njivi Makpelskoj prema Mamriji u zemlji Hananskoj, koju kupi Avram s njivom u Efrona Hetejina da ima svoj grob.
31 A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
Ondje pogreboše Avrama i Saru ženu njegovu, ondje pogreboše Isaka i Reveku ženu njegovu, i ondje pogreboh Liju.
32 Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
A kupljena je njiva i peæina na njoj u sinova Hetovijeh.
33 Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.
A kad izgovori Jakov zapovjesti sinovima svojim, diže noge svoje na postelju, i umrije, i pribran bi k rodu svojemu.

< Farawa 49 >