< Farawa 49 >
1 Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
And Jacob calleth unto his sons and saith, 'Be gathered together, and I declare to you that which doth happen with you in the latter end of the days.
2 “Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
'Be assembled, and hear, sons of Jacob, And hearken unto Israel your father.
3 “Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
Reuben! my first-born thou, My power, and beginning of my strength, The abundance of exaltation, And the abundance of strength;
4 Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
Unstable as water, thou art not abundant; For thou hast gone up thy father's bed; Then thou hast polluted: My couch he went up!
5 “Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
Simeon and Levi [are] brethren! Instruments of violence — their espousals!
6 Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
Into their secret, come not, O my soul! Unto their assembly be not united, O mine honour; For in their anger they slew a man, And in their self-will eradicated a prince.
7 La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
Cursed [is] their anger, for [it is] fierce, And their wrath, for [it is] sharp; I divide them in Jacob, And I scatter them in Israel.
8 “Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
Judah! thou — thy brethren praise thee! Thy hand [is] on the neck of thine enemies, Sons of thy father bow themselves to thee.
9 Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
A lion's whelp [is] Judah, For prey, my son, thou hast gone up; He hath bent, he hath crouched as a lion, And as a lioness; who causeth him to arise?
10 Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
The sceptre turneth not aside from Judah, And a lawgiver from between his feet, Till his Seed come; And his [is] the obedience of peoples.
11 Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
Binding to the vine his ass, And to the choice vine the colt of his ass, He hath washed in wine his clothing, And in the blood of grapes his covering;
12 Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
Red [are] eyes with wine, And white [are] teeth with milk!
13 “Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
Zebulun at a haven of the seas doth dwell, And he [is] for a haven of ships; And his side [is] unto Zidon.
14 “Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
Issacher [is] a strong ass, Crouching between the two folds;
15 Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
And he seeth rest that [it is] good, And the land that [it is] pleasant, And he inclineth his shoulder to bear, And is to tribute a servant.
16 “Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
Dan doth judge his people, As one of the tribes of Israel;
17 Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
Dan is a serpent by the way, An adder by the path, Which is biting the horse's heels, And its rider falleth backward.
18 “Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
For Thy salvation I have waited, Jehovah!
19 “Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
Gad! a troop assaulteth him, But he assaulteth last.
20 “Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
Out of Asher his bread [is] fat; And he giveth dainties of a king.
21 “Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
Naphtali [is] a hind sent away, Who is giving beauteous young ones.
22 “Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
Joseph [is] a fruitful son; A fruitful son by a fountain, Daughters step over the wall;
23 Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
And embitter him — yea, they have striven, Yea, hate him do archers;
24 Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
And his bow abideth in strength, And strengthened are the arms of his hands By the hands of the Mighty One of Jacob, Whence is a shepherd, a son of Israel.
25 saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
By the God of thy father who helpeth thee, And the Mighty One who blesseth thee, Blessings of the heavens from above, Blessings of the deep lying under, Blessings of breasts and womb; —
26 Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
Thy father's blessings have been mighty Above the blessings of my progenitors, Unto the limit of the heights age-during They are for the head of Joseph, And for the crown of the one Separate [from] his brethren.
27 “Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
Benjamin! a wolf teareth; In the morning he eateth prey, And at evening he apportioneth spoil.'
28 Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
All these [are] the twelve tribes of Israel, and this [is] that which their father hath spoken unto them, and he blesseth them; each according to his blessing he hath blessed them.
29 Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
And he commandeth them, and saith unto them, 'I am being gathered unto my people; bury me by my fathers, at the cave which [is] in the field of Ephron the Hittite;
30 kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
in the cave which [is] in the field of Machpelah, which [is] on the front of Mamre, in the land of Canaan, which Abraham bought with the field from Ephron the Hittite for a possession of a burying-place;
31 A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
(there they buried Abraham and Sarah his wife; there they buried Isaac and Rebekah his wife; and there I buried Leah);
32 Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
the purchase of the field and of the cave which [is] in it, [is] from Sons of Heth.'
33 Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.
And Jacob finisheth commanding his sons, and gathereth up his feet unto the bed, and expireth, and is gathered unto his people.