< Farawa 49 >

1 Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
Derpaa kaldte Jakob sine Sønner til sig og sagde: »Saml eder, saa vil jeg forkynde eder, hvad der skal hændes eder i de sidste Dage:
2 “Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
Kom hid og hør, Jakobs Sønner, lyt til eders Fader Israel!
3 “Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
Ruben, du er min førstefødte, min Styrke og min Mandskrafts første, ypperst i Højhed, ypperst i Kraft!
4 Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
Du skummer over som Vandet, men du mister din Forret; thi du besteg din Faders Leje. Skændigt handled du da han besteg mit Leje!
5 “Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
Simeon og Levi, det Broder Par, Voldsredskaber er deres Vaaben.
6 Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
I deres Raad giver min Sjæl ej Møde, i deres Forsamling tager min Ære ej Del; thi i Vrede dræbte de Mænd, egenraadigt lamslog de Okser.
7 La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
Forbandet være deres Vrede, saa vild den er, deres Hidsighed, saa voldsom den er! Jeg spreder dem i Jakob, splitter dem ad i Israel!
8 “Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
Juda, dig skal dine Brødre prise, din Haand skal gribe dine Fjender i Nakken, din Faders Sønner skal bøje sig for dig.
9 Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
En Løveunge er Juda. Fra Rov stiger du op, min Søn! Han ligger og strækker sig som en Løve, ja, som en Løvinde, hvo tør vække ham!
10 Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
Ikke viger Kongespir fra Juda, ej Herskerstav fra hans Fødder, til han, hvem den tilhører; kommer, ham skal Folkene lyde.
11 Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
Han binder sit Æsel ved Vinstokken, ved Ranken Asenindens Fole, tvætter i Vin sin Kjortel, sin Kappe i Drueblod,
12 Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
med Øjnene dunkle af Vin og Tænderne hvide af Mælk!
13 “Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
Zebulon har hjemme ved Havets Kyst, han bor ved Skibenes Kyst, hans Side er vendt mod Zidon.
14 “Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
Issakar, det knoglede Æsel, der strækker sig mellem Foldene,
15 Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
fandt Hvilen sød og Landet lifligt; derfor bøjed han Ryg under Byrden og blev en ufri Træl.
16 “Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
Dan dømmer sit Folk saa godt som nogen Israels Stamme.
17 Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
Dan blive en Slange ved Vejen, en Giftsnog ved Stien, som bider Hesten i Hælen, saa Rytteren styrter bagover! —
18 “Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
Paa din Frelse bier jeg, HERRE!
19 “Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
Gad, paa ham gør Krigerskarer Indhug, men han gør Indhug i Hælene paa dem.
20 “Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
Aser, hans Føde er fed, Lækkerier for Konger har han at give.
21 “Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
Naftali er en løssluppen Hind, han fremfører yndig Tale.
22 “Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
Et yppigt Vintræ er Josef, et yppigt Vintræ ved Kilden, Ranker slynger sig over Muren.
23 Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
Bueskytter fejder imod ham, strides med ham, gør Angreb paa ham,
24 Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
men hans Bue er stærk, hans Hænders Arme rappe; det kommer fra Jakobs Vældige, fra Hyrden, Israels Klippe,
25 saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
fra din Faders Gud — han hjælpe dig! Og Gud den Almægtige, han velsigne dig med Himmelens Velsignelser oventil og Dybets Velsignelser nedentil, med Brysters og Moderlivs Velsignelser!
26 Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
Din Faders Velsignelser overgaar de ældgamle Bjerges Velsignelser, de evige Højes Herlighed. Maatte de komme over Josefs Hoved, over Issen paa Fyrsten blandt Brødre!
27 “Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
Benjamin, den rovlystne Ulv, om Morgenen æder han Rov, om Aftenen deler han Bytte!«
28 Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
Alle disse er Israels Stammer, tolv i Tal, og det var, hvad deres Fader talte til dem, og han velsignede dem, hver især af dem gav han sin særlige Velsignelse.
29 Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
Og han sagde til dem som sin sidste Vilje: »Nu samles jeg til mit Folk; jord mig da hos mine Fædre i Hulen paa Hetiten Efrons Mark,
30 kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
i Hulen paa Makpelas Mark over for Mamre i Kana'ans Land, den Mark, som Abraham købte af Hetiten Efron til Gravsted,
31 A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
hvor de jordede Abraham og hans Hustru Sara, hvor de jordede Isak og hans Hustru Rebekka, og hvor jeg jordede Lea.
32 Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
Marken og Hulen derpaa blev købt af Hetiterne.«
33 Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.
Dermed havde Jakob givet sine Sønner sin Vilje til Kende, og han strakte sine Fødder ud paa Lejet, udaandede og samledes til sin Slægt.

< Farawa 49 >