< Farawa 49 >

1 Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
Povolal pak Jákob synů svých, a řekl: Sejděte se, a oznámím vám, co se s vámi díti bude potomních dnů.
2 “Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
Shromažďte se a slyšte synové Jákobovi, poslyšte Izraele otce svého.
3 “Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
Ruben, prvorozený můj jsi ty, síla má, a počátek moci mé, vyvýšenost důstojenství a vyvýšenost síly.
4 Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
Prudce sběhneš jako voda. Nebudeš vyvýšen, proto že jsi vstoupil na lůže otce svého; a jakž jsi poškvrnil postele mé, zmizelo vyvýšení tvé.
5 “Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
Simeon a Léví bratří, nástrojové nepravosti jsou v příbytcích jejich.
6 Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
Do tajné rady jejich nevcházej duše má, k shromáždění jejich nepřipojuj se slávo má; nebo v prchlivosti své zbili muže, a svévolně vyvrátili zed.
7 La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
Zlořečená prchlivost jejich, nebo neustupná; i hněv jejich, nebo zatvrdilý jest. Rozdělím je v Jákobovi, a rozptýlím je v Izraeli.
8 “Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
Judo, ty jsi, tebe chváliti budou bratří tvoji; ruka tvá bude na šíji nepřátel tvých; klaněti se budou tobě synové otce tvého.
9 Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
Lvíče Juda, z loupeže, synu můj, vrátil jsi se; schýliv se, ležel jako lev a jako lvice; kdo zbudí ho?
10 Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
Nebude odjata berla od Judy, ani vydavatel zákona od noh jeho, dokudž nepřijde Sílo; a k němu se shromáždí národové.
11 Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
Uváže k vinnému kmenu osle své, a k výbornému kmenu oslátko oslice své. Práti bude u víně roucho své, a v červeném víně oděv svůj.
12 Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
Èervenějších očí bude nad víno, a zubů bělejších nad mléko.
13 “Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
Zabulon bydliti bude na břehu mořském, a na přístavu lodí, a pomezí jeho až k Sidonu.
14 “Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
Izachar osel silný, ležící mezi dvěma břemeny.
15 Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
A vida odpočinutí, že jest dobré, a zemi, že jest rozkošná, sehne rameno své k nošení, a dávati bude daně.
16 “Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
Dan souditi bude lid svůj, jako jedno z pokolení Izraelských.
17 Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
Budeť Dan jako had podlé cesty, jako had rohatý podlé stezky, štípaje kopyta koně, aby spadl jezdec jeho zpět.
18 “Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
Spasení tvého očekávám, ó Hospodine!
19 “Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
Gád, vojsko přemůže jej, však on svítězí potom.
20 “Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
Asser, tučný bude pokrm jeho, a onť vydávati bude rozkoše královské.
21 “Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
Neftalím jako laň vypuštěná, vydávaje výmluvnosti krásné.
22 “Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
Ratolest rostoucí Jozef, ratolest rostoucí podlé studnice; ratolesti vycházely nad zed.
23 Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
Ačkoli hořkostí naplnili jej, a stříleli na něj, a v tajné nenávisti měli ho střelci:
24 Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
Však zůstalo v síle lučiště jeho, a zsilila se ramena rukou jeho z rukou mocného Jákobova; odkudž byl pastýř a kámen Izraelův;
25 saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
Od silného Boha, jemuž sloužil otec tvůj, kterýž spomáhá tobě, a od všemohoucího, kterýž požehná tobě požehnáními nebeskými s hůry, požehnáními propasti ležící hluboko, požehnáním prsů a života.
26 Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
Požehnání otce tvého silnější budou nad požehnání předků mých, až k končinám pahrbků věčných; budou nad hlavou Jozefovou, a na vrchu hlavy Nazarejského mezi bratřími jeho.
27 “Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
Beniamin, vlk dravý, ráno bude jísti loupež, a večer rozdělí kořisti.
28 Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
Všech těchto pokolení Izraelských jest dvanácte; a to jest, což mluvil jim otec jejich; požehnal jim také, jednomu každému vedlé požehnání jeho požehnal.
29 Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
A poroučeje jim, řekl: Já připojen budu k lidu svému; pochovejte mne s otci mými v jeskyni té, kteráž jest na poli Efrona Hetejského,
30 kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
V jeskyni, kteráž jest na poli Machpelah, jenž jest naproti Mamre v zemi Kananejské, kterouž koupil Abraham spolu s polem tím od Efrona Hetejského k dědičnému pohřbu.
31 A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
Tam pochovali Abrahama a Sáru ženu jeho; tam pochovali Izáka a Rebeku ženu jeho; tam také pochovali Líu.
32 Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
Koupeno pak bylo pole a jeskyně, kteráž na něm, od synů Het.
33 Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.
A když přestal Jákob přikazovati synům svým, složil nohy své na ložci a umřel; a připojen jest k lidu svému.

< Farawa 49 >