< Farawa 48 >
1 Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi.
Poslije javiše Josifu: eno, otac ti je bolestan. A on povede sa sobom dva sina svoja, Manasiju i Jefrema.
2 Sa’ad da aka faɗa wa Yaƙub, “Ɗanka Yusuf ya zo gare ka,” sai Isra’ila ya ƙoƙarta ya tashi ya zauna a kan gado.
I javiše Jakovu i rekoše: evo sin tvoj Josif ide k tebi. A Izrailj se okrijepi, te sjede na postelji svojoj.
3 Yaƙub ya ce wa Yusuf, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan’ana, a can ya albarkace ni
I reèe Jakov Josifu: Bog svemoguæi javi se meni u Luzu u zemlji Hananskoj, i blagoslovi me;
4 ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
I reèe mi: uèiniæu te da narasteš i namnožiš se; i uèiniæu od tebe mnoštvo naroda, i daæu zemlju ovu sjemenu tvojemu nakon tebe da je njihova dovijeka.
5 “To, yanzu,’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
Sada dakle dva sina tvoja, što ti se rodiše u zemlji Misirskoj prije nego doðoh k tebi u Misir, moji su, Jefrem i Manasija kao Ruvim i Simeun neka budu moji.
6 Duk waɗansu’ya’yan da aka haifa maka bayansu za su zama naka; a yankin da suka gāda za a lissafa a ƙarƙashin sunayen’yan’uwansu.
A djeca koju rodiš poslije njih, neka budu tvoja i neka se po imenu braæe svoje zovu u našljedstvu svojem.
7 Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya,’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem).
Jer kad se vratih iz Padana, umrije mi Rahilja u zemlji Hananskoj na putu, kad bješe još malo do Efrate; i pogreboh je na putu u Efratu, a to je Vitlejem.
8 Sa’ad da Isra’ila ya ga’ya’yan Yusuf maza, sai ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan?”
A vidjev Izrailj sinove Josifove, reèe: ko su ovi?
9 Yusuf ya ce wa mahaifinsa, “Su ne’ya’yan da Allah ya ba ni a nan.” Sa’an nan Isra’ila ya ce, “Kawo mini su saboda in albarkace su.”
A Josif reèe ocu svojemu: moji sinovi, koje mi Bog dade ovdje. A on reèe: dovedi ih k meni, da ih blagoslovim.
10 Yanzu fa idanun Isra’ila sun fara rasa ƙarfi saboda tsufa, har ba ya iya gani sosai. Saboda haka Yusuf ya kawo’ya’yansa maza kusa da shi, sai mahaifinsa ya sumbace su ya rungume su.
A oèi bjehu Izrailju otežale od starosti, te ne mogaše dobro vidjeti. A kad mu ih privede, cjeliva ih i zagrli.
11 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ban yi tsammani zan ga fuskarka kuma ba, yanzu kuwa Allah ya bar ni in ga’ya’yanka su ma.”
I reèe Izrailj Josifu: nijesam mislio da æu vidjeti lice tvoje; a gle, Bog mi dade da vidim i porod tvoj.
12 Sa’an nan Yusuf ya ɗauke su daga gwiwoyin Isra’ila ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
A Josif odmaèe ih od koljena njegovijeh i pokloni se licem do zemlje.
13 Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi.
Pa ih uze Josif obojicu, Jefrema sebi s desne strane a Izrailju s lijeve, Manasiju pak sebi s lijeve strane a Izrailju s desne; i tako ih primaèe k njemu.
14 Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa.
A Izrailj pruživ desnu ruku svoju metnu je na glavu Jefremu mlaðemu, a lijevu na glavu Manasiji, tako namjestiv ruke navlaš, ako i jest Manasija bio prvenac.
15 Sa’an nan ya albarkaci Yusuf ya ce, “Bari Allah a gaban wanda kakannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allahn da ya zama makiyayina dukan raina zuwa wannan rana,
I blagoslovi Josifa govoreæi: Bog, kojemu su svagda ugaðali oci moji Avram i Isak, Bog, koji me je hranio otkako sam postao do današnjega dana,
16 Mala’ikan da ya cece ni daga dukan cuta bari yă albarkaci samarin nan. Bari a kira su da sunana da sunayen kakannina Ibrahim da Ishaku bari kuma su ƙaru ƙwarai a bisa duniya.”
Anðeo, koji me je izbavljao od svakoga zla, da blagoslovi djecu ovu, i da se po mojemu imenu i po imenu otaca mojih Avrama i Isaka prozovu, i da se kao ribe namnože na zemlji!
17 Sa’ad da Yusuf ya ga mahaifinsa yana sa hannun damansa a kan Efraim bai ji daɗi ba; saboda haka ya ɗauke hannun mahaifinsa ya cire shi daga kan Efraim zuwa kan Manasse.
A Josif kad vidje gdje otac metnu desnu ruku svoju na glavu Jefremu, ne bi mu milo, pa uhvati za ruku oca svojega da je premjesti s glave Jefremove na glavu Manasijinu.
18 Yusuf ya ce masa, “A’a, mahaifina, wannan shi ne ɗan farin; ka sa hannunka na dama a kansa.”
I reèe Josif ocu svojemu: ne tako, oèe; ovo je prvenac, metni desnicu njemu na glavu.
19 Amma mahaifinsa ya ƙi ya ce, “Na sani, ɗana, na sani. Shi ma zai zama mutane, zai kuma zama mai girma. Duk da haka ɗan’uwansa zai zama mai girma fiye da shi, kuma zuriyarsa za tă zama ƙungiyar al’ummai.”
Ali otac njegov ne htje, nego reèe: znam, sine, znam; i od njega æe postati narod, i on æe biti velik; ali æe mlaði brat njegov biti veæi od njega, i sjeme æe njegovo biti veliko mnoštvo naroda.
20 Ya albarkace su a wannan rana ya ce, “A cikin sunanku Isra’ila zai sa wannan albarka ‘Bari Allah yă sa ku zama kamar Efraim da Manasse.’” Saboda haka ya sa Efraim gaban Manasse.
I blagoslovi ih u onaj dan i reèe: tobom æe Izrailj blagosiljati govoreæi: Bog da te uèini kao Jefrema i kao Manasiju. Tako postavi Jefrema pred Manasiju.
21 Sa’an nan Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ina gab da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku
Poslije reèe Izrailj Josifu: evo ja æu skoro umrijeti; ali æe Bog biti s vama i odvešæe vas opet u zemlju otaca vaših.
22 Kuma gare ka, a matsayi wanda yake kan’yan’uwanka, na ba da gonar da na karɓe daga Amoriyawa da takobi da kuma bakana.”
I ja ti dajem jedan dio više nego braæi tvojoj, koji uzeh iz ruku Amorejskih maèem svojim i lukom svojim.