< Farawa 48 >

1 Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi.
After these deades tydiges were brought vnto Ioseph: that his father was seke. And he toke with him his ij. sones Manasses and Ephraim.
2 Sa’ad da aka faɗa wa Yaƙub, “Ɗanka Yusuf ya zo gare ka,” sai Isra’ila ya ƙoƙarta ya tashi ya zauna a kan gado.
Then was it sayde vnto Iacob: beholde thy sonne Ioseph commeth vnto the. And Israel toke his strength vnto him and satt vp on the bedd
3 Yaƙub ya ce wa Yusuf, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan’ana, a can ya albarkace ni
and sayde vnto Ioseph: God all mightie appeared vnto me at lus in the lande of Canaan ad blessed me
4 ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
and sayde vnto me: beholde I will make the growe and will multiplye the and will make a great nombre of people of the and will geue this lande vnto the and vnto thy seed after ye vnto an euerlastinge possession.
5 “To, yanzu,’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
Now therfore thy. ij. sones Manasses ad Ephraim which were borne vnto the before I came to the in to Egipte shalbe myne: euen as Ruben and Simeo shall they be vnto me.
6 Duk waɗansu’ya’yan da aka haifa maka bayansu za su zama naka; a yankin da suka gāda za a lissafa a ƙarƙashin sunayen’yan’uwansu.
And the childern which thou getest after them shalbe thyne awne: but shalbe called with the names of their brethern in their enheritaunces.
7 Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya,’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem).
And after I came from Mesopotamia Rahel dyed apon my hande in the lande of Canaa by the waye: when I had but a feldes brede to goo vnto Ephrat. And I buried her there in ye waye to Ephrat which is now called Bethlehem.
8 Sa’ad da Isra’ila ya ga’ya’yan Yusuf maza, sai ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan?”
And Israel behelde Iosephes sonnes and sayde: what are these?
9 Yusuf ya ce wa mahaifinsa, “Su ne’ya’yan da Allah ya ba ni a nan.” Sa’an nan Isra’ila ya ce, “Kawo mini su saboda in albarkace su.”
And Ioseph sayde vnto his father: they are my sonnes which God hath geuen me here. And he sayde: brynge them to me and let me blesse them.
10 Yanzu fa idanun Isra’ila sun fara rasa ƙarfi saboda tsufa, har ba ya iya gani sosai. Saboda haka Yusuf ya kawo’ya’yansa maza kusa da shi, sai mahaifinsa ya sumbace su ya rungume su.
And the eyes of Israell were dymme for age so that he coude not see. And he broughte them to him ad he kyssed the and embraced them.
11 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ban yi tsammani zan ga fuskarka kuma ba, yanzu kuwa Allah ya bar ni in ga’ya’yanka su ma.”
And Israel sayde vnto Ioseph: I had not thoughte to haue sene thy face and yet loo God hath shewed it me and also thy seed.
12 Sa’an nan Yusuf ya ɗauke su daga gwiwoyin Isra’ila ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And Ioseph toke them awaye from his lappe and they fell on the grounde before him.
13 Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi.
Than toke Ioseph them both: Ephraim in his ryghte hande towarde Israels left hande ad Manasses in his left hande towarde Israels ryghte hande and brought them vnto him.
14 Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa.
And Israel stretched out his righte hande and layde it apon Ephraims head which was the yonger and his lyft hade apon Manasses heed crossinge his handes for manasses was the elder.
15 Sa’an nan ya albarkaci Yusuf ya ce, “Bari Allah a gaban wanda kakannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allahn da ya zama makiyayina dukan raina zuwa wannan rana,
And he blessed Ioseph saynge: God before whome my fathers Abraham and Isaac dyd walke and the God which hath fedd me all my life longe vnto this daye
16 Mala’ikan da ya cece ni daga dukan cuta bari yă albarkaci samarin nan. Bari a kira su da sunana da sunayen kakannina Ibrahim da Ishaku bari kuma su ƙaru ƙwarai a bisa duniya.”
And the angell which hath delyuered me fro all euyll blesse these laddes: yt they maye be called after my name and after my father Abraham and Isaac and that they maye growe ad multiplie apo the erth.
17 Sa’ad da Yusuf ya ga mahaifinsa yana sa hannun damansa a kan Efraim bai ji daɗi ba; saboda haka ya ɗauke hannun mahaifinsa ya cire shi daga kan Efraim zuwa kan Manasse.
When Ioseph sawe that his father layd his ryghte hande apon the heade of Ephraim it displeased him. And he lifte vpp his fathers hade to haue removed it from Ephraims head vnto Manasses head
18 Yusuf ya ce masa, “A’a, mahaifina, wannan shi ne ɗan farin; ka sa hannunka na dama a kansa.”
and sayde vnto his father: Not so my father for this is the eldest. Put thy right hande apon his head.
19 Amma mahaifinsa ya ƙi ya ce, “Na sani, ɗana, na sani. Shi ma zai zama mutane, zai kuma zama mai girma. Duk da haka ɗan’uwansa zai zama mai girma fiye da shi, kuma zuriyarsa za tă zama ƙungiyar al’ummai.”
And his father wold not but sayde: I knowe it well my sonne I knowe it well. He shalbe also a people ad shalbe great. But of a troth his yonger brother shalbe greatter than he and his seed shall be full of people.
20 Ya albarkace su a wannan rana ya ce, “A cikin sunanku Isra’ila zai sa wannan albarka ‘Bari Allah yă sa ku zama kamar Efraim da Manasse.’” Saboda haka ya sa Efraim gaban Manasse.
And he blessed them sainge. At the ensample of these the Israelites shall blesse and saye: God make the as Ephraim and as Manasses. Thus sett he Ephraim before Manasses.
21 Sa’an nan Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ina gab da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku
And Israel sayde vnto Ioseph: beholde I dye. And god shalbe with you and bringe you agayne vnto the land of youre fathers.
22 Kuma gare ka, a matsayi wanda yake kan’yan’uwanka, na ba da gonar da na karɓe daga Amoriyawa da takobi da kuma bakana.”
Moreouer I geue vnto the a porcyon of lande aboue thy brethern which I gatt out of the handes of the Amorites with my swerde and wyth my bowe.

< Farawa 48 >