< Farawa 48 >
1 Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi.
And it came to pass after these things, that one said to Joseph, Lo! thy father, is sick. So he took his two sons with him, Manasseh and Ephraim.
2 Sa’ad da aka faɗa wa Yaƙub, “Ɗanka Yusuf ya zo gare ka,” sai Isra’ila ya ƙoƙarta ya tashi ya zauna a kan gado.
And one told Jacob, and said—Lo! thy son Joseph, coming in unto thee. So Israel strengthened himself, and sat up on the couch.
3 Yaƙub ya ce wa Yusuf, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan’ana, a can ya albarkace ni
Then said Jacob unto Joseph, GOD Almighty, appeared unto me in Luz in the land of Canaan, —and blessed me;
4 ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
and said unto me—Behold me! about to make thee fruitful, so will I multiply thee, and give thee to become a multitude of peoples, —so will I give this land to thy seed after thee, as an age-abiding possession.
5 “To, yanzu,’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
Now, therefore thy two sons who were born to thee in the land of Egypt, before I came in unto thee in Egypt, are mine! Ephraim and Manasseh, like Reuben and Simeon, shall be mine!
6 Duk waɗansu’ya’yan da aka haifa maka bayansu za su zama naka; a yankin da suka gāda za a lissafa a ƙarƙashin sunayen’yan’uwansu.
But thine offspring which thou hast begotten after them, thine own shall they be, —after the name of their brethren, shall they be called in their inheritance.
7 Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya,’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem).
But, as for me, when I came in from Padan, Rachel died by me, in the land of Canaan, in the way, while yet there was a stretch of country to come into Ephrath, —so I buried her there in the way to Ephrath, the same, is Bethlehem.
8 Sa’ad da Isra’ila ya ga’ya’yan Yusuf maza, sai ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan?”
Then Israel saw Joseph’s sons, —and said—Who are these?
9 Yusuf ya ce wa mahaifinsa, “Su ne’ya’yan da Allah ya ba ni a nan.” Sa’an nan Isra’ila ya ce, “Kawo mini su saboda in albarkace su.”
And Joseph said unto his father, My sons, they are, whom God hath given me, in this place. And he said—Bring them, I pray thee, unto me, that I may bless them.
10 Yanzu fa idanun Isra’ila sun fara rasa ƙarfi saboda tsufa, har ba ya iya gani sosai. Saboda haka Yusuf ya kawo’ya’yansa maza kusa da shi, sai mahaifinsa ya sumbace su ya rungume su.
Now, the eyes of Israel, had become dim from old age, —he could not see, —so he drew them near unto him, and kissed them, and embraced them.
11 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ban yi tsammani zan ga fuskarka kuma ba, yanzu kuwa Allah ya bar ni in ga’ya’yanka su ma.”
And Israel said unto Joseph, To see thine own face, had I not thought, —and lo! God hath caused me to see even thy seed!
12 Sa’an nan Yusuf ya ɗauke su daga gwiwoyin Isra’ila ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And Joseph brought them out from beside his knees, and bowed himself down with his face towards the earth.
13 Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi.
And Joseph took them both, —Ephraim in his right hand on Israel’s left hand, and Manasseh in his left hand, on Israel’s right hand, and drew them near unto him.
14 Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa.
Then Israel put forth his right hand and laid it upon the head of Ephraim, though, he, was the younger, and his left hand upon the head of Manasseh, —crossing his hands, although, Manasseh, was the first-born.
15 Sa’an nan ya albarkaci Yusuf ya ce, “Bari Allah a gaban wanda kakannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allahn da ya zama makiyayina dukan raina zuwa wannan rana,
Thus blessed he Joseph, and said, —God himself—before whom walked my fathers. Abraham and Isaac, God himself—who hath been my shepherd, since I came into being until this day; —
16 Mala’ikan da ya cece ni daga dukan cuta bari yă albarkaci samarin nan. Bari a kira su da sunana da sunayen kakannina Ibrahim da Ishaku bari kuma su ƙaru ƙwarai a bisa duniya.”
The Messenger—who hath been my redeemer from all evil—bless the lads! And may there be called upon them, my name, and the name of my fathers. Abraham and Isaac; And may they swarm into a multitude, in the midst of the earth!
17 Sa’ad da Yusuf ya ga mahaifinsa yana sa hannun damansa a kan Efraim bai ji daɗi ba; saboda haka ya ɗauke hannun mahaifinsa ya cire shi daga kan Efraim zuwa kan Manasse.
And Joseph saw that his father had laid his right hand on the head of Ephraim and it was displeasing in his eyes, —so he took hold of his father’s hand to remove it from off the head of Ephraim, on to the head of Manasseh.
18 Yusuf ya ce masa, “A’a, mahaifina, wannan shi ne ɗan farin; ka sa hannunka na dama a kansa.”
And Joseph said unto his father—Not so, my father! for, this, is the firstborn, lay thy right hand upon his head.
19 Amma mahaifinsa ya ƙi ya ce, “Na sani, ɗana, na sani. Shi ma zai zama mutane, zai kuma zama mai girma. Duk da haka ɗan’uwansa zai zama mai girma fiye da shi, kuma zuriyarsa za tă zama ƙungiyar al’ummai.”
And his father refused, and said—I know—my son, I know! He also, shall become a people, and he also, shall become great, —but nevertheless, his younger brother, shall become greater than he, and his seed, shall become a filling up of the nations.
20 Ya albarkace su a wannan rana ya ce, “A cikin sunanku Isra’ila zai sa wannan albarka ‘Bari Allah yă sa ku zama kamar Efraim da Manasse.’” Saboda haka ya sa Efraim gaban Manasse.
And he blessed them on that day, saying—In thee, let Israel bless himself saying, God set thee as Ephraim, and as Manasseh! So he set Ephraim before Manasseh.
21 Sa’an nan Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ina gab da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku
And Israel said unto Joseph: Lo! I, am about to die, —but it shall come to pass that, God will be with you, and will take you back into the land of your fathers.
22 Kuma gare ka, a matsayi wanda yake kan’yan’uwanka, na ba da gonar da na karɓe daga Amoriyawa da takobi da kuma bakana.”
But, I, have given to thee one mountain-track above thy brethren, —which I took out of the hand of the Amorite, with my sword and with my bow.