< Farawa 48 >

1 Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi.
And it came to pass after these things, that one told Joseph, Behold, thy father is sick. And he took with him his two sons Manasseh and Ephraim.
2 Sa’ad da aka faɗa wa Yaƙub, “Ɗanka Yusuf ya zo gare ka,” sai Isra’ila ya ƙoƙarta ya tashi ya zauna a kan gado.
And one told Jacob and said, Behold, thy son Joseph is coming to thee. And Israel strengthened himself, and sat upon the bed.
3 Yaƙub ya ce wa Yusuf, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan’ana, a can ya albarkace ni
And Jacob said to Joseph, The Almighty God appeared to me at Luz in the land of Canaan, and blessed me,
4 ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
and he said to me, Behold, I will make thee fruitful and multiply thee, and I will make of thee a company of peoples; and will give this land to thy seed after thee [for] an everlasting possession.
5 “To, yanzu,’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
And now thy two sons, who were born to thee in the land of Egypt before I came to thee into Egypt, shall be mine: Ephraim and Manasseh shall be mine, as Reuben and Simeon.
6 Duk waɗansu’ya’yan da aka haifa maka bayansu za su zama naka; a yankin da suka gāda za a lissafa a ƙarƙashin sunayen’yan’uwansu.
And thy family which thou hast begotten after them shall be thine: they shall be called after the name of their brethren in their inheritance.
7 Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya,’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem).
And as for me, when I came from Padan, Rachel died by me in the land of Canaan on the way, when there was yet a certain distance to come to Ephrath; and I buried her there on the way to Ephrath, that is, Bethlehem.
8 Sa’ad da Isra’ila ya ga’ya’yan Yusuf maza, sai ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan?”
And Israel beheld Joseph's sons, and said, Who are these?
9 Yusuf ya ce wa mahaifinsa, “Su ne’ya’yan da Allah ya ba ni a nan.” Sa’an nan Isra’ila ya ce, “Kawo mini su saboda in albarkace su.”
And Joseph said to his father, They are my sons, whom God has given me here. And he said, Bring them, I pray thee, to me, that I may bless them.
10 Yanzu fa idanun Isra’ila sun fara rasa ƙarfi saboda tsufa, har ba ya iya gani sosai. Saboda haka Yusuf ya kawo’ya’yansa maza kusa da shi, sai mahaifinsa ya sumbace su ya rungume su.
But the eyes of Israel were heavy from age: he could not see. And he brought them nearer to him; and he kissed them, and embraced them.
11 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ban yi tsammani zan ga fuskarka kuma ba, yanzu kuwa Allah ya bar ni in ga’ya’yanka su ma.”
And Israel said to Joseph, I had not thought to see thy face; and behold, God has let me see also thy seed.
12 Sa’an nan Yusuf ya ɗauke su daga gwiwoyin Isra’ila ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And Joseph brought them out from his knees, and bowed down with his face to the earth.
13 Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi.
And Joseph took them both, Ephraim in his right hand toward Israel's left hand, and Manasseh in his left hand toward Israel's right hand, and brought [them] near to him.
14 Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa.
But Israel stretched out his right hand, and laid [it] on Ephraim's head — now he was the younger — and his left hand on Manasseh's head; guiding his hands intelligently, for Manasseh was the firstborn.
15 Sa’an nan ya albarkaci Yusuf ya ce, “Bari Allah a gaban wanda kakannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allahn da ya zama makiyayina dukan raina zuwa wannan rana,
And he blessed Joseph, and said, The God before whom my fathers Abraham and Isaac walked, the God that shepherded me all my life long to this day,
16 Mala’ikan da ya cece ni daga dukan cuta bari yă albarkaci samarin nan. Bari a kira su da sunana da sunayen kakannina Ibrahim da Ishaku bari kuma su ƙaru ƙwarai a bisa duniya.”
the Angel that redeemed me from all evil, bless the lads; and let my name be named upon them, and the name of my fathers Abraham and Isaac; and let them grow into a multitude in the midst of the land!
17 Sa’ad da Yusuf ya ga mahaifinsa yana sa hannun damansa a kan Efraim bai ji daɗi ba; saboda haka ya ɗauke hannun mahaifinsa ya cire shi daga kan Efraim zuwa kan Manasse.
When Joseph saw that his father laid his right hand on the head of Ephraim, it was evil in his eyes; and he took hold of his father's hand to remove it from Ephraim's head to Manasseh's head.
18 Yusuf ya ce masa, “A’a, mahaifina, wannan shi ne ɗan farin; ka sa hannunka na dama a kansa.”
And Joseph said to his father, Not so, my father, for this is the firstborn: put thy right hand on his head.
19 Amma mahaifinsa ya ƙi ya ce, “Na sani, ɗana, na sani. Shi ma zai zama mutane, zai kuma zama mai girma. Duk da haka ɗan’uwansa zai zama mai girma fiye da shi, kuma zuriyarsa za tă zama ƙungiyar al’ummai.”
But his father refused and said, I know, my son, I know: he also will become a people, and he also will be great; but truly his younger brother will be greater than he; and his seed will become the fulness of nations.
20 Ya albarkace su a wannan rana ya ce, “A cikin sunanku Isra’ila zai sa wannan albarka ‘Bari Allah yă sa ku zama kamar Efraim da Manasse.’” Saboda haka ya sa Efraim gaban Manasse.
And he blessed them that day, saying, In thee will Israel bless, saying, God make thee as Ephraim and Manasseh! And he set Ephraim before Manasseh.
21 Sa’an nan Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ina gab da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku
And Israel said to Joseph, Behold, I die; and God will be with you, and bring you again to the land of your fathers.
22 Kuma gare ka, a matsayi wanda yake kan’yan’uwanka, na ba da gonar da na karɓe daga Amoriyawa da takobi da kuma bakana.”
And I have given to thee one tract [of land] above thy brethren, which I took out of the hand of the Amorite with my sword and with my bow.

< Farawa 48 >