< Farawa 48 >
1 Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi.
Efter disse Begivenheder fik Josef Melding om, at hans Fader var syg. Da tog han sine Sønner, Manasse og Efraim, med sig.
2 Sa’ad da aka faɗa wa Yaƙub, “Ɗanka Yusuf ya zo gare ka,” sai Isra’ila ya ƙoƙarta ya tashi ya zauna a kan gado.
Da det nu meldtes Jakob, at hans Søn Josef var kommet, tog Israel sig sammen og satte sig oprejst paa Lejet.
3 Yaƙub ya ce wa Yusuf, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan’ana, a can ya albarkace ni
Jakob sagde til Josef: »Gud den Almægtige aabenbarede sig for mig i Luz i Kana'ans Land og velsignede mig;
4 ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
og han sagde til mig: Jeg vil gøre dig frugtbar og give dig et talrigt Afkom og gøre dig til en Mængde Stammer, og jeg vil give dit Afkom efter dig Land til evigt Eje!
5 “To, yanzu,’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
Nu skal dine to Sønner, der er født dig i Ægypten før mit komme til dig her i Ægypten, være mine, Efraim og Manasse skal være mine saa godt som Ruben og Simeon;
6 Duk waɗansu’ya’yan da aka haifa maka bayansu za su zama naka; a yankin da suka gāda za a lissafa a ƙarƙashin sunayen’yan’uwansu.
derimod skal de Børn, du har faaet efter dem, være dine; men de skal nævnes efter deres Brødres Navne i deres Arvelod.
7 Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya,’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem).
Da jeg kom fra Paddan, døde Rakel for mig, medens jeg var undervejs i Kana'an, da vi endnu var et stykke Vej fra Efrat, og jeg jordede hende der paa Vejen til Efrat, det er Betlehem«.
8 Sa’ad da Isra’ila ya ga’ya’yan Yusuf maza, sai ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan?”
Da Israel saa Josefs Sønner, sagde han: »Hvem bringer du der?«
9 Yusuf ya ce wa mahaifinsa, “Su ne’ya’yan da Allah ya ba ni a nan.” Sa’an nan Isra’ila ya ce, “Kawo mini su saboda in albarkace su.”
Josef svarede sin Fader: »Det er mine Sønner, som Gud har skænket mig her.« Da sagde han: »Bring dem hen til mig, at jeg kan velsigne dem!«
10 Yanzu fa idanun Isra’ila sun fara rasa ƙarfi saboda tsufa, har ba ya iya gani sosai. Saboda haka Yusuf ya kawo’ya’yansa maza kusa da shi, sai mahaifinsa ya sumbace su ya rungume su.
Men Israels Øjne var svækkede af Alderdom, saa at han ikke kunde se. Da førte han dem hen til ham, og han kyssede og omfavnede dem.
11 Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ban yi tsammani zan ga fuskarka kuma ba, yanzu kuwa Allah ya bar ni in ga’ya’yanka su ma.”
Og Israel sagde til Josef: »Jeg havde ikke turdet haabe at faa dit Ansigt at se, og nu har Gud endog ladet mig se dit Afkom!«
12 Sa’an nan Yusuf ya ɗauke su daga gwiwoyin Isra’ila ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Derpaa tog Josef dem bort fra hans Knæ og kastede sig til Jorden paa sit Ansigt.
13 Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi.
Josef tog saa dem begge, Efraim i sin højre Haand til venstre for Israel og Manasse i sin venstre Haand til højre for Israel, og førte dem hen til ham;
14 Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa.
men Israel udrakte sin højre Haand og lagde den paa Efraims Hoved, uagtet han var den yngste, og sin venstre Haand lagde han paa Manasses Hoved, saa at han lagde Hænderne over Kors; thi Manasse var den førstefødte.
15 Sa’an nan ya albarkaci Yusuf ya ce, “Bari Allah a gaban wanda kakannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allahn da ya zama makiyayina dukan raina zuwa wannan rana,
Derpaa velsignede han Josef og sagde: »Den Gud, for hvis Aasyn mine Fædre Abraham og Isak vandrede, den Gud, der har vogtet mig: fra min første Færd og til nu,
16 Mala’ikan da ya cece ni daga dukan cuta bari yă albarkaci samarin nan. Bari a kira su da sunana da sunayen kakannina Ibrahim da Ishaku bari kuma su ƙaru ƙwarai a bisa duniya.”
den Engel, der har udløst mig fra alt ondt, velsigne Drengene, saa at mit Navn og mine Fædre Abrahams og Isaks Navn maa blive nævnet ved dem, og de maa vokse i Mængde i Landet!«
17 Sa’ad da Yusuf ya ga mahaifinsa yana sa hannun damansa a kan Efraim bai ji daɗi ba; saboda haka ya ɗauke hannun mahaifinsa ya cire shi daga kan Efraim zuwa kan Manasse.
Men da Josef saa, at hans Fader lagde sin højre Haand paa Efraims Hoved, var det ham imod, og han greb sin Faders Haand for at tage den bort fra Efraims Hoved og lægge den paa Manasses;
18 Yusuf ya ce masa, “A’a, mahaifina, wannan shi ne ɗan farin; ka sa hannunka na dama a kansa.”
og Josef sagde til sin Fader: »Nej, ikke saaledes, Fader, thi denne er den førstefødte; læg din højre Haand paa hans Hoved!«
19 Amma mahaifinsa ya ƙi ya ce, “Na sani, ɗana, na sani. Shi ma zai zama mutane, zai kuma zama mai girma. Duk da haka ɗan’uwansa zai zama mai girma fiye da shi, kuma zuriyarsa za tă zama ƙungiyar al’ummai.”
Men hans Fader vægrede sig og sagde: »Jeg ved det, min Søn, jeg ved det! Ogsaa han skal blive til et Folk, ogsaa han skal blive stor; men hans yngre Broder skal blive større end han, og hans Afkom skal blive en Mangfoldighed af Folkeslag!«
20 Ya albarkace su a wannan rana ya ce, “A cikin sunanku Isra’ila zai sa wannan albarka ‘Bari Allah yă sa ku zama kamar Efraim da Manasse.’” Saboda haka ya sa Efraim gaban Manasse.
Saaledes velsignede han dem paa den Dag og sagde: »Med eder skal Israel velsigne og sige: Gud gøre dig som Efraim og Manasse!« Og han stillede Efraim foran Manasse.
21 Sa’an nan Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ina gab da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku
Da sagde Israel til Josef: »Jeg skal snart dø, men Gud skal være med eder og føre eder tilbage til eders Fædres Land.
22 Kuma gare ka, a matsayi wanda yake kan’yan’uwanka, na ba da gonar da na karɓe daga Amoriyawa da takobi da kuma bakana.”
Dig giver jeg ud over dine Brødre en Højderyg, som jeg har fravristet Amoriterne med mit Sværd og min Bue!«