< Farawa 47 >

1 Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
Yusuf gidip firavuna, “Babamla kardeşlerim davarları, sığırları ve bütün eşyalarıyla Kenan ülkesinden geldiler” diye haber verdi, “Şu anda Goşen bölgesindeler.”
2 Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
Sonra kardeşlerinden beşini seçerek firavunun huzuruna çıkardı.
3 Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
Firavun Yusuf'un kardeşlerine, “Ne iş yapıyorsunuz?” diye sordu. “Biz kulların atalarımız gibi çobanız” diye yanıtladılar,
4 Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
“Bu ülkeye geçici bir süre için geldik. Çünkü Kenan ülkesinde şiddetli kıtlık var. Davarlarımız için otlak bulamıyoruz. İzin ver, Goşen bölgesine yerleşelim.”
5 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
Firavun Yusuf'a, “Babanla kardeşlerin yanına geldiler” dedi,
6 ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
“Mısır ülkesi senin sayılır. Onları ülkenin en iyi yerine yerleştir. Goşen bölgesine yerleşsinler. Sence aralarında becerikli olanlar varsa, davarlarıma bakmakla görevlendir.”
7 Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
Yusuf babası Yakup'u getirip firavunun huzuruna çıkardı. Yakup firavunu kutsadı.
8 sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
Firavun, Yakup'a, “Kaç yaşındasın?” diye sordu.
9 Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
Yakup, “Gurbet yıllarım yüz otuz yılı buldu” diye yanıtladı, “Ama yıllar çabuk ve zorlu geçti. Atalarımın gurbet yılları kadar uzun sürmedi.”
10 Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
Sonra firavunu kutsayıp huzurundan ayrıldı.
11 Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
Yusuf babasıyla kardeşlerini Mısır'a yerleştirdi; firavunun buyruğu uyarınca onlara ülkenin en iyi yerinde, Ramses bölgesinde mülk verdi.
12 Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
Ayrıca babasıyla kardeşlerine ve babasının ev halkına, sahip oldukları çocukların sayısına göre yiyecek sağladı.
13 A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
Kıtlık öyle şiddetlendi ki, hiçbir ülkede yiyecek bulunmaz oldu. Mısır ve Kenan ülkeleri kıtlıktan kırılıyordu.
14 Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
Yusuf sattığı buğdaya karşılık Mısır ve Kenan'daki bütün paraları toplayıp firavunun sarayına götürdü.
15 Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
Mısır ve Kenan'da para tükenince Mısırlılar Yusuf'a giderek, “Bize yiyecek ver” dediler, “Gözünün önünde ölelim mi? Paramız bitti.”
16 Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
Yusuf, “Paranız bittiyse, davarlarınızı getirin” dedi, “Onlara karşılık size yiyecek vereyim.”
17 Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
Böylece davarlarını Yusuf'a getirdiler. Yusuf atlara, davar ve sığır sürülerine, eşeklere karşılık onlara yiyecek verdi. Bir yıl boyunca hayvanlarına karşılık onlara yiyecek sağladı.
18 Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
O yıl geçince, ikinci yıl yine geldiler. Yusuf'a, “Efendim, gerçeği senden saklayacak değiliz” dediler, “Paramız tükendi, davarlarımızı da sana verdik. Canımızdan ve toprağımızdan başka verecek bir şeyimiz kalmadı.
19 Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
Gözünün önünde ölelim mi? Toprağımız çöle mi dönsün? Canımıza ve toprağımıza karşılık bize yiyecek sat. Toprağımızla birlikte firavunun kölesi olalım. Bize tohum ver ki ölmeyelim, yaşayalım; toprak da çöle dönmesin.”
20 Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
Böylece Yusuf Mısır'daki bütün toprakları firavun için satın aldı. Mısırlılar'ın hepsi tarlalarını sattılar, çünkü kıtlık onları buna zorluyordu. Toprakların tümü firavunun oldu.
21 Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
Yusuf Mısır'ın bir ucundan öbür ucuna kadar bütün halkı köleleştirdi.
22 Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
Yalnız kâhinlerin toprağını satın almadı. Çünkü onlar firavundan aylık alıyor, firavunun bağladığı aylıkla geçiniyorlardı. Bu yüzden topraklarını satmadılar.
23 Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
Yusuf halka, “Sizi de toprağınızı da firavun için satın aldım” dedi, “İşte size tohum, toprağı ekin.
24 Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
Ürün devşirdiğinizde, beşte birini firavuna vereceksiniz. Beşte dördünü ise tohumluk olarak kullanacak ve ailelerinizle, çocuklarınızla yiyeceksiniz.”
25 Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
“Canımızı kurtardın” diye karşılık verdiler, “Efendimizin gözünde lütuf bulalım. Firavunun kölesi oluruz.”
26 Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
Yusuf ürünün beşte birinin firavuna verilmesini Mısır'da toprak yasası yaptı. Bu yasa bugün de yürürlüktedir. Yalnız kâhinlerin toprağı firavuna verilmedi.
27 To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
İsrail Mısır'da Goşen bölgesine yerleşti. Orada mülk sahibi oldular, çoğalıp arttılar.
28 Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
Yakup Mısır'da on yedi yıl yaşadı. Ömrü toplam yüz kırk yedi yıl sürdü.
29 Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
Ölümü yaklaşınca, oğlu Yusuf'u çağırıp, “Eğer benden hoşnut kaldınsa, lütfen elini uyluğumun altına koy” dedi, “Bana sevgi ve sadakat göstereceğine söz ver. Lütfen beni Mısır'da gömme.
30 amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
Atalarıma kavuştuğum zaman beni Mısır'dan çıkarıp onların yanına göm.” Yusuf, “Dediğin gibi yapacağım” diye karşılık verdi.
31 Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.
İsrail, “Ant iç” dedi. Yusuf ant içti. İsrail yatağının başı ucunda eğilip RAB'be tapındı.

< Farawa 47 >