< Farawa 47 >
1 Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
Potem je prišel Jožef in povedal faraonu ter rekel: »Moj oče, moji bratje, njihovi tropi, njihove črede in vse, kar imajo, so prišli iz kánaanske dežele. Glej, v gošenski deželi so.«
2 Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
Vzel je nekatere izmed svojih bratov, pet mož in jih predstavil faraonu.
3 Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
Faraon je njegovim bratom rekel: »Kakšen je vaš poklic?« Faraonu so odgovorili: »Tvoji služabniki so pastirji, tako mi, kakor tudi naši očetje.«
4 Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
Poleg tega so faraonu rekli: »Zato smo prišli, da začasno prebivamo v deželi, kajti tvoji služabniki nimajo pašnika za svoje trope, kajti huda lakota je v kánaanski deželi. Sedaj te torej prosimo, naj tvoji služabniki prebivajo v gošenski deželi.«
5 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
Faraon je Jožefu spregovoril, rekoč: »Tvoj oče in tvoji bratje so prišli k tebi.
6 ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
Egiptovska dežela je pred teboj. V najboljši deželi pripravi svojemu očetu in bratom, da prebivajo. V gošenski deželi naj prebivajo in če poznaš med njimi katerekoli marljive ljudi, potem jih naredi gospodarje nad mojo živino.«
7 Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
Jožef je privedel svojega očeta Jakoba in ga postavil pred faraona in Jakob je blagoslovil faraona.
8 sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
Faraon je Jakobu rekel: »Koliko si star?«
9 Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
Jakob je faraonu rekel: »Dni let mojega popotovanja je sto trideset let. Malo in zli so bili dnevi let mojega življenja in nisem dosegel dni let življenja svojih očetov v dneh njihovega popotovanja.«
10 Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
Jakob je blagoslovil faraona in odšel izpred faraona.
11 Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
Jožef je namestil svojega očeta in svoje brate ter jim dal posest v egiptovski deželi, v najboljšem delu dežele, v Ramesésovi deželi, kakor je faraon zapovedal.
12 Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
Jožef je vzdrževal svojega očeta, svoje brate in vso družino svojega očeta s kruhom, glede na njihove družine.
13 A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
In ni bilo kruha v vsej deželi, kajti lakota je bila zelo huda, tako da je egiptovska dežela in vsa kánaanska dežela zaradi lakote slabela.
14 Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
Jožef je zbral ves denar, ki se je našel v egiptovski deželi in v kánaanski deželi, za žito, ki so ga kupovali. In Jožef je denar prinesel v faraonovo hišo.
15 Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
Ko pa je v egiptovski deželi in v kánaanski deželi zmanjkalo denarja, so vsi Egipčani prišli k Jožefu in rekli: »Daj nam kruha, kajti zakaj bi umrli v tvoji prisotnosti? Kajti denarja je zmanjkalo.«
16 Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
Jožef je rekel: »Dajte svojo živino in jaz vam bom dal za vašo živino, če je denarja zmanjkalo.«
17 Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
Svojo živino so privedli k Jožefu in Jožef jim je dal kruha v zameno za konje in za trope in za živino od čred in za osle in to leto jih je nahranil s kruhom za vso njihovo živino.
18 Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
Ko je bilo to leto končano, so prišli k njemu drugo leto in mu rekli: » Tega ne bomo skrivali pred mojim gospodom, da je naš denar porabljen. Moj gospod ima tudi naše črede in živino. Sploh ni veliko ostalo v očeh mojega gospoda, razen naših teles in naših zemljišč.
19 Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
Zakaj bi umrli pred tvojimi očmi, tako mi kakor naša dežela? Kupi nas in našo deželo za kruh, pa bomo mi in naša dežela služabniki faraonu. Daj nam seme, da bomo lahko živeli in ne umrli, da dežela ne bo zapuščena.«
20 Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
Jožef je vso egiptovsko deželo kupil za faraona, kajti Egipčani so prodali vsak človek svoje polje, ker je nad njimi prevladala lakota in tako je dežela postala faraonova.
21 Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
Kar se tiče ljudstva, jih je premestil v mesta, od enega konca egiptovskih meja, celo do drugega njegovega konca.
22 Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
Samo zemljišč duhovnikov ni pokupil, kajti duhovniki so imeli od faraona njim določen delež in jedli svoj delež, ki jim ga je faraon dajal, zato svojih zemljišč niso prodali.
23 Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
Potem je Jožef rekel ljudstvu: »Glejte, danes sem kupil vas in vašo deželo za faraona. Glejte, tukaj je seme za vas in vi boste posejali deželo.
24 Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
Z donosom se bo zgodilo, da boste peti del dali faraonu, štirje deli pa bodo vaši lastni, za seme polja in za vašo hrano in za tiste iz vaših družin in za hrano za vaše malčke.«
25 Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
Rekli so: »Rešil si naša življenja. Naj najdemo milost v očeh mojega gospoda, mi pa bomo faraonovi služabniki.«
26 Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
Jožef je to naredil v egiptovski deželi [za] zakon do današnjega dne, da bo imel faraon peti del, razen dežele duhovnikov, ki ni postala faraonova.
27 To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
Izrael je prebival v egiptovski deželi, v pokrajini Gošen in v njej so imeli posesti in rastli ter se silno pomnožili.
28 Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
Jakob je v egiptovski deželi živel sedemnajst let. Tako je bila celotna Jakobova starost sto sedeminštirideset let.
29 Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
Približal se je čas, ko je Izrael moral umreti in poklical je svojega sina Jožefa ter mu rekel: »Če sem sedaj našel milost v tvojem pogledu, položi, prosim te, svojo roko pod moje stegno ter z menoj postopaj dobrotljivo in iskreno. Ne pokoplji me, prosim te, v Egiptu,
30 amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
temveč hočem ležati s svojimi očeti in ti me boš odnesel iz Egipta in me pokopal na njihovem grobišču.« Rekel je: »Storil bom kakor si rekel.«
31 Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.
Rekel je: »Prisezi mi.« In prisegel mu je. In Izrael se je priklonil na vzglavju postelje.