< Farawa 47 >
1 Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
Så kom Josef og meldte dette til Farao og sa: Min far og mine brødre er kommet hit fra Kana'ans land med sitt småfe og storfe og alt det de har; og nu er de i Gosen.
2 Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
Og av alle sine brødre tok han ut fem og fremstilte dem for Farao.
3 Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
Da sa Farao til hans brødre: Hvad er eders levevei? De svarte Farao: Dine tjenere er fehyrder, vi som våre fedre.
4 Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
Så sa de til Farao: Vi er kommet for å bo en tid her i landet; for dine tjenere hadde ikke beite for sin buskap, fordi det er en hård hungersnød i Kana'ans land; la derfor dine tjenere få bo i landet Gosen!
5 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
Da sa Farao til Josef: Din far og dine brødre er kommet til dig.
6 ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
Egyptens land ligger åpent for dig; la din far og dine brødre bo i den beste del av landet, la dem bo i Gosen! Og dersom du vet at det er dyktige menn iblandt dem, da sett dem til opsynsmenn over min buskap!
7 Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
Og Josef førte Jakob, sin far, inn og fremstilte ham for Farao; og Jakob velsignet Farao.
8 sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
Og Farao spurte Jakob: Hvor mange er dine leveår?
9 Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
Jakob svarte Farao: Min utlendighets år er hundre og tretti år; få og onde har mine leveår vært, og de har ikke nådd mine fedres leveår i deres utlendighets tid.
10 Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
Og Jakob velsignet Farao, og så gikk han ut fra Farao.
11 Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
Og Josef lot sin far og sine brødre bosette sig og gav dem eiendom i Egyptens land, i den beste del av landet, i landet Ra'amses, således som Farao hadde pålagt ham.
12 Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
Og Josef forsørget sin far og sine brødre og hele sin fars hus med brød efter barnas tall.
13 A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
Og det fantes ikke brød i hele landet; for hungersnøden var meget hård, så Egyptens land og Kana'ans land vansmektet av hunger.
14 Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
Og Josef samlet alle de penger som fantes i Egyptens land og i Kana'ans land; han fikk dem for det korn de kjøpte, og Josef la pengene op i Faraos hus.
15 Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
Men da det var forbi med pengene i Egyptens land og i Kana'ans land, da kom alle egypterne til Josef og sa: Gi oss brød! Hvorfor skal vi dø for dine øine? Vi har ikke flere penger.
16 Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
Og Josef sa: Kom hit med eders buskap, så vil jeg gi eder brød for eders buskap, dersom I ikke har flere penger.
17 Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
Så kom de til Josef med sin buskap, og Josef gav dem brød for hestene og for småfeet og storfeet som de hadde, og for asenene, og han holdt dem med brød det år for hele deres buskap.
18 Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
Så gikk det år til ende, og året efter kom de til ham og sa: Vi vil ikke dølge for min herre at det er forbi med pengene, og buskapen som vi eide, har min herre fått; det er intet tilbake for min herre uten vårt legeme og vår jord.
19 Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
Hvorfor skal vi gå til grunne for dine øine, både vi og vår jord? Kjøp oss og vår jord for brød, så skal vi med vår jord være Faraos træler; og gi oss såkorn, så vi kan leve og ikke skal dø, og jorden ikke legges øde.
20 Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
Så kjøpte Josef all jorden i Egypten til Farao; for egypterne solgte hver sin jordvei, fordi hungersnøden trykket dem hårdt; og landet blev Faraos eiendom.
21 Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
Men folket flyttet han om i byene, fra den ene ende av Egyptens land til den andre.
22 Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
Bare prestenes jord kjøpte han ikke; for Farao hadde gitt prestene faste inntekter, og de levde av sine faste inntekter, som Farao hadde gitt dem; derfor solgte de ikke sin jord.
23 Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
Og Josef sa til folket: Nu har jeg kjøpt eder og eders jord til Farao; se, her har I såkorn, tilså nu jorden!
24 Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
Og når avgrøden kommer inn, da skal I gi en femtedel til Farao, og de fire deler skal I ha til utsæd på eders akrer og til føde for eder og dem som er i eders hus, og til føde for eders barn.
25 Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
Da sa de: Du har holdt oss i live; la oss finne nåde for min herres øine, så skal vi være Faraos træler.
26 Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
Så satte Josef dette som en lov - og den lov gjelder den dag idag for jorden i Egypten - at Farao skulde ha femtedelen; bare Prestenes jord blev ikke Faraos eiendom.
27 To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
Israel blev boende i Egyptens land, i landet Gosen. og de fikk sig eiendom der og var fruktbare og blev meget tallrike.
28 Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
Og Jakob levde i Egyptens land i sytten år; og Jakobs dager, hans leveår, blev hundre og syv og firti år.
29 Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
Da det led mot den tid at Israel skulde dø, kalte han sin sønn Josef til sig og sa til ham: Kjære, har jeg funnet nåde for dine øine, så legg din hånd under min lend og vis mig den kjærlighet og trofasthet at du ikke begraver mig i Egypten,
30 amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
men la mig få hvile hos mine fedre, før mig bort fra Egypten og legg mig i deres grav! Og han svarte: Jeg skal gjøre som du sier.
31 Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.
Da sa han: Tilsverg mig det! Og han tilsvor ham det. Og Israel bøide sig ned over hodegjerdet i sengen og tilbad.