< Farawa 47 >

1 Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
Tad Jāzeps nāca un pasludināja Faraonam un sacīja: mans tēvs un mani brāļi un viņu sīkie lopi un viņu vērši un viss, kas tiem pieder, ir atnākuši no Kanaāna zemes, un redzi, tie ir Gošenes zemē.
2 Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
Un viņš ņēma piecus no visiem saviem brāļiem, un tos veda Faraona priekšā.
3 Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
Un Faraons sacīja uz viņa brāļiem: kas ir jūsu darbs? Un tie sacīja uz Faraonu: tavi kalpi ir lopu gani, tā pat mēs kā mūsu tēvi. Un tie sacīja uz Faraonu:
4 Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
Mēs esam nākuši šinī zemē piemist, jo ganības trūkst tiem sīkiem lopiem, kas taviem kalpiem pieder, jo bads ir grūts Kanaāna zemē, un nu vēli, lūdzams, lai tavi kalpi apmetās Gošenes zemē.
5 Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
Tad Faraons runāja uz Jāzepu un sacīja: tavs tēvs un tavi brāļi pie tevis atnākuši.
6 ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
Ēģiptes zeme stāv tev atvērā; lai tavs tēvs un tavi brāļi dzīvo tai vislabākā zemes vietā, - lai tie mīt Gošenes zemē, un ja tu zini, ka starp tiem ir krietni vīri, tad iecel tos par manu lopu uzraugiem.
7 Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
Un Jāzeps atveda savu tēvu Jēkabu, un to stādīja Faraona priekšā, un Jēkabs svētīja Faraonu.
8 sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
Un Faraons sacīja uz Jēkabu: Cik gadu tavām dzīvības dienām?
9 Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
Tad Jēkabs sacīja uz Faraonu: manas svešniecības gadu dienas ir simts un trīsdesmit gadi; īsas un grūtas ir bijušas manas dzīvības gadu dienas un nepanāk manu tēvu gadus viņu svešniecības dienās.
10 Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
Un Jēkabs svētīja Faraonu un izgāja no Faraona.
11 Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
Un Jāzeps savam tēvam un saviem brāļiem iedeva mājas vietas, un tiem deva Ēģiptes zemē to labāko zemes vietu turēt, Raēmzes tiesā, tā kā Faraons bija pavēlējis.
12 Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
Un Jāzeps uzturēja savu tēvu un savus brāļus un visu sava tēva namu ar maizi, kā kuram bija bērnu.
13 A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
Un pa visām zemēm nebija maizes; jo bads bija ļoti grūts, tā ka Ēģiptes zemē un Kanaāna zemē aiz bada nevarēja glābties.
14 Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
Un Jāzeps sakrāja visu naudu, kas atradās Ēģiptes zemē un Kanaāna zemē par to labību, ko tie pirka, un Jāzeps to naudu nesa Faraona namā.
15 Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
Kad nu tā nauda Ēģiptes zemē un Kanaāna zemē bija pagalam, tad visi ēģiptieši nāca pie Jāzepa un sacīja: dod mums maizes, kādēļ mums tavā priekšā būs mirt, kad naudas vairs nav?
16 Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
Tad Jāzeps sacīja: dodiet savus lopus; tad es jums došu par jūsu lopiem, kad naudas nav.
17 Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
Tad tie veda savus lopus pie Jāzepa, un Jāzeps tiem deva maizes par zirgiem un par sīkiem lopiem un par vēršiem un par ēzeļiem, un viņš tos to gadu izmitināja ar maizi par visiem viņu lopiem.
18 Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
Kad tas gads bija galā, tad tie otrā gadā pie viņa nāca un uz viņu sacīja: mēs neapslēpsim priekš sava kunga, ka nevien tā nauda ir beigta, bet arī tie lopi mūsu kungam ir kļuvuši un nekas nav atlicis priekš mūsu kunga, kā vien mūsu miesas un mūsu tīrumi.
19 Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
Kādēļ mums būs bojā iet priekš tavām acīm, mums un mūsu tīrumiem? Pērc mūs un mūsu tīrumus par maizi, tad mēs ar savu tīrumu Faraonam būsim par kalpiem, un dodi sēklu, ka mēs dzīvojam un nemirstam, un mūsu zeme nepaliek tukša.
20 Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
Tad Jāzeps visus ēģiptiešu tīrumus pirka priekš Faraona, jo ēģiptieši pārdeva ikviens savu tīrumu, tāpēc ka bads tiem bija grūts.
21 Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
Tad tā zeme kļuva Faraona rokā, un viņš tos ļaudis pārcēla pilsētās, no viena Ēģiptes robežu gala līdz otram galam.
22 Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
Tikai priesteru tīrumus viņš nepirka, jo priesteriem bija sava daļa no Faraona, un tie ēda no savas daļas, ko Faraons tiem deva, tādēļ tie savu tīrumu nepārdeva.
23 Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
Tad Jāzeps sacīja uz tiem ļaudīm: redzi, es šodien jūs un jūsu tīrumus esmu pircis Faraonam, redzi, še jums sēkla, ka jūs tīrumus apsējat.
24 Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
Bet ar augļiem tas tā būs, ka jūs piekto tiesu dodat Faraonam, un četras daļas jums piederēs, tīrumus apsēt un par pārtiku jums un tiem, kas jūsu namā, un par pārtiku jūsu bērniņiem.
25 Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
Un tie sacīja: tu mūs esi uzturējis dzīvus; lai žēlastību atrodam sava kunga acīs, tad mēs būsim Faraona kalpi.
26 Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
Tad Jāzeps to iecēla par likumu pār ēģiptiešu tīrumiem līdz šai dienai, ka Faraonam tā piektā tiesa nāktos, - tikai priesteru zeme vien nekļuva Faraonam.
27 To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
Un Israēls mita Ēģiptē Gošenes zemē, un tur uzturējās un auga un vairojās ļoti.
28 Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
Un Jēkabs dzīvoja Ēģiptes zemē septiņpadsmit gadus, un Jēkaba dienas bija simts četrdesmit un septiņi gadi.
29 Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
Kad nu Israēla laiks pienāca, ka tam bija mirt, tad viņš sauca savu dēlu Jāzepu un uz to sacīja: ja es tavās acīs esmu atradis žēlastību, tad liec jel lūdzams savu roku apakš manas ciskas un dari pie manis žēlastību un patiesību: neaproc jel mani Ēģiptes zemē;
30 amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
Bet es gribu gulēt pie saviem tēviem; un tev būs mani izvest no Ēģiptes un mani aprakt viņu kapos, - un tas sacīja: es darīšu pēc tava vārda.
31 Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.
Tad viņš sacīja: zvērē man. Un tas viņam zvērēja. Un Israēls pielūdza Dievu savas gultas galvgalā.

< Farawa 47 >